‘Yan majalisar dokokin kasar Iran sun kada kuri’ar tsige ministan harkokin tattalin arziki da kudi Abdonnasser Hemmati daga mukaminsa saboda matsalolin tattalin arziki da kuma faduwar darajar kudin kasar.

Hemmati ya rasa kuri’ar amincewa a zaman majalisar na wannan Lahadi inda ‘yan majalisa 182 daga cikin 273 suka kada kuri’ar tsige shi.

‘Yan majalisa tamanin da tara ne suka bukaci ya ci gaba da zama a kan mukaminsa.

A yayin Zaman ministan da kansa da shugaban kasar Masoud Pezeshkian sun halarci wurin, yayin da kuma ‘yan majalisar kan batun kudurin, amma dai kudirin ya wuce bayan samun rinjayen amincewa da shi.

Shugaba Pezeshkian ya kare Hemmati, tsohon gwamnan babban bankin kasar Iran, ya kuma ce kasar na cikin yakin tattalin arziki da makiya, kuma zargin juna ba zai magance wata matsala ba.

Ya jaddada cewa hadin kai da hadin gwiwa ne kadai mafita ga matsalolin da kasar ke fuskanta.

Hemmati ya kuma yi jawabi a zaman inda ya ce Iran na da karfin iko kuma za ta yi nasara a yakin tattalin arzikin makiya.

Wasu gungun ‘yan majalisa 91 ne suka fara shirin tsige Hemmati, saboda gazawarsa wajen daidaita kasuwanni da kuma dakile hauhawar farashin kayayyaki.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: tattalin arziki

এছাড়াও পড়ুন:

Kwamitin Neman Sabuwar Karamar Hukumar Kanya Babba Ya Gabatar Da Takardar Bukatarsa Ga Majalisar Dattawa

Kwamitin neman sabuwar Karamar Hukumar Kanya Babba daga Karamar Hukumar Babura ta Jihar Jigawa, ya gabatar da takardar bukatarsa ga kwamitin Majalisar Dattawa mai kula da kirkiro jihohi da kananan hukumomi a zaman da aka yi a jihar Kano.

A yayin mika takardar, Shugaban kwamitin kuma Hakimin Kanya Babba,  Makaman Ringim, Malam Mohammed Ibrahim ya bayyana cewar wannan yunkuri ya bi duk sharuddan da kundin tsarin mulki ya shimfida don kafa sabuwar karamar hukuma.

 

Makaman na Ringim ya kara da cewar, daukacin al’ummar yankin Kanya Babba, ciki da wajen mazabar na matukar goyon bayan hakan domin bunkasa ci gaban tattalin arziki da al’umma a yankin.

Da yake karbar takardar, Shugaban kwamitin Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibril, ya nuna jin dadin sa da jajircewar mutanen Kanya Babba wajen mika takardar.

Barau Jibrin, ya kuma tabbatar musu kwamitinsa zai yi adalci da gaskiya a aikin da aka dora musa.

Wakilinmu ya bamu rahoton cewar, taron mika bukatar ya samu halartar mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Injiniya Aminu Usman da Sanatan Jigawa ta Arewa maso Yamma, Alhaji Babangida Husaini da dan majalisar jiha mai wakiltar mazabar Kanya, Alhaji Ibrahim Hashim Kanya da shugaban Karamar Hukumar Babura, Alhaji Hamisu Muhammad Garu da mai bawa gwamna shawara kan harkokin bada aiyukan kwangila Usman Haladu Isa da Alhaji Salisu Muazu Kanya da hakimai da Dagatai da ‘yan siyasa da kuma sauran masu ruwa da tsaki da dimbin masoya.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
  • Kwamitin Neman Sabuwar Karamar Hukumar Kanya Babba Ya Gabatar Da Takardar Bukatarsa Ga Majalisar Dattawa
  • Za mu halasta kafa ƙasar Falasɗinu muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba — Birtaniya
  • Muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba za mu amince da kafa ƙasar Falasɗinu — Birtaniya
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Na Da Kwamitoci 30 Da Ke Sa Ido Kan Ma’aikatun Gwamnati
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
  •  Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta
  • Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa
  • An fara shigar da kayan agaji a Gaza