Sojoji sun ƙwato makamai a dajin Sambisa
Published: 2nd, March 2025 GMT
Dakarun Sojin Najeriya tare da haɗin gwiwar JTF na Operation Hadin Kai, sun kai farmaki dajin Sambisa, inda suka ƙwato makamai da alburusai masu yawa.
Wata majiya ta bayyana cewa sojojin, sun kai samame yankin Ukuba tare da bataliya ta musamman ta 199 da kuma ‘yan sandan JTF domin bincike da ƙwato makaman da ‘yan ta’adda suka ɓoye.
Da suka isa wajen da misalin ƙarfe 12:10 na rana a ranar 1 ga watan Maris, sun tarar da cewa ‘yan ta’addan sun tsere, inda suka bar makamai da kayan yaƙi da dama, ciki har da injina daban-daban, bindigogi, bututun RPG, da wasu kayayyakin fashewa.
Sojoji sun ce wannan farmakin yana daga cikin matakan da suke ɗauka domin fatattakar ragowar ‘yan ta’adda daga dajin Sambisa da kuma ƙwato makaman da suka ɓoye a yankin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan ta adda
এছাড়াও পড়ুন:
Ta yi wa saurayinta ƙaryar shekarunta 27 maimakon 47
Wani saurayi ya wallafa wani labarinsa a kafar sada zumunta ta Reddit tare da yin nadama, inda ya ce matar da suke soyayya ta faɗa masa cewa, an haife ta ne a shekarar 1998, har sai da ya duba bayanan fasfo dinta.
A wani lamari mai ban al’ajabi da ban tsoro, matashin ɗan shekara 26 ya girgiza bayan ya gano cewa, matar da yake soyayya da ita da nufin aure, bayan shafe shekaru huɗu suna tare tana da shekara 47, ba 27 ba, kamar yadda ta yi iƙirari.
An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da Portugal Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a ChibokSaurayin ya tafi shafin Reddit don ya wallafa labarinsa na nadama, inda ya ce, matar ta sha gaya masa cewa, an haife ta ne a watan Afrilun 1998, amma ya gano an haife ta a 1977 shekara 48 ke nan.
Saurayin ya rubuta a cikin shafin intanet cewa, “ina soyayya tare da budurwata har tsawon shekaru 4, kuma koyaushe tana ikirarin an haife ta a watan Afrilu ‘1998, amma na gano a ainihin lokacin da aka haife ta shi ne 1977.
Saurayin ya ce, ba shi da wani dalili na yin shakku, domin matar ta yi kama da ’yar shekara 27, ba wanda ya taba tunanin ta kusa 50 ba, amma ya yarda cewa akwai wasu alamomi a tsawon tafiyar soyayyar.
“Akwai wasu alamomi a lokacin da muke tare, amma na zabi in yi watsi da su tunda ba ni da gogewa kan gano ainihin (wannan ita ce alakar soyayya ta ta farko mai tsawo),” in ji shi, inda ya kara da cewa, matar ta damu da kamanninta, kuma duk kawayenta sun fi shekara 27 sosai.
“Duk lokacin da na nemi ta nuna min wasu takardu kamar fasfo sai ta ƙi nuna min, ta ba da uzuri na banza da kokarin kauce wa batun.”
A yayin binciken, saurayin ya kuma sami hoton gwajin ciki, wanda ’yan watanni kafin su hadu kuma su fara soyayya.
Kafofin sada zumunta na zamani sun mayar da martani kan batun, yayin da sakonni suka yi ta yaduwa, daruruwan mutane sun sharhi, inda akasari ke fada wa mutumin ya kawo karshen dangantakarsa da matar da aka gina ta bisa karya.