HausaTv:
2025-09-18@03:39:30 GMT

Nijar: An Kashe Sojoji 11 A Wani Hari Na Kungiyar al-Ka’ida

Published: 2nd, March 2025 GMT

Rahotanni da suke fitowa daga Nijar sun bayyana cewa; Wata kungiyar mai alaka da al-ka’ida ta  dauki alhakin kashe sojojin kasar 11 a kan iyaka da Aljeriya.

A ranar Juma’ar da ta gabata ne dai lamarin ya faru,kuma a jiya Asabar ne aka yi jana’izarsu a garin Agadez, kamar yadda wata majiyar watsa labara ta jamhuriyar Nijar ta ambata.

Shafin “Air Info” da ya watsa laabrin ya kuma ce; Jami’an soja da dama sun hjalarci jana’izar sojojin da su ka kwanta dama, daga cikinsu har da janar Musa Salih Barmo, babban hafsan hafsoshin sojan kasar.

Tashar Radiyo din kasar ta Nijar ta ce, an yi wa sojojin kwanton bauna ne a lokacin da suke sintiri akan  mahadar iyakaokin kasar, da Mali da kuma Burkina Faso.

Labarin Radiyon ya kuma ce, Janar Barmo ya nufi asibitin garin Agadez din domin yin dubiyar sojojin da su ka jikkata.”

 A gefe daya wata kungiyar mai  suna; “Nasratul-Islam Wal Muslimin” da reshe ne na alka’ida, ta dauki alhakin kai harin.

A lokuta da dama a baya sojojin na jamhuriyar Nijar sun sha fuskantar hare-hare irin wadannan, sai dai ba kasafai kungiyoyin da suke ikirarin jihadi suke daukar alhakin kai wa ba.

Saharar dake Arewacin Nijar tana da girma kuma tana kusa da kasar Libya da masu hada-hadar mutane da kuma  ‘yan hijira suke bi suna ratsawa domin shiga cikin kasashen turai.

Kungiyar “Ikilid” wacce ba ta gwamnati ba da take sa ido akan duk wasu rikice-rikice da suke faruwa a duniya, ta ce daga 2023 zuwa yanzu an kashe mutane 2400 a cikin wannan kasa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

Yarjejeniyar, a cewar daukacin mahalarta taron, ta nuna wani gagarumin mataki na kawo karshen tashe-tashen hankula, garkuwa da mutane da satar shanu a Arewa maso Yamma, da kuma yankin Arewa.

 

Yarjejeniyar wacce Mai Maradin Katsina da Hakimin Kurfi, Alhaji Mansur Amadu Kurfi, da shugaban karamar hukumar, Babangida Abdullahi Kurfi suka shirya, ta gudana ne a dajin Wurma, inda ake fama da rashin tsaro.

 

Manyan jagororin ‘yan bindigan da suka hada da Alhaji Usman Kachalla Ruga da Sani Muhindinge da Yahaya Sani (Hayyu) da kuma Alhaji Shu’aibu duk sun yi alkawarin tsagaita wuta.

 

Daga baya suka sako mutanen da suka kama kuma suka bar manoma su koma gonakansu ba tare da wata barazana ba.

 

Sai dai kasa da wata guda da kulla yarjejeniyar, an tattaro cewa ‘yan bindigar sun sake kai hari a Zamfara inda suka yi awon gaba da masallata da dama.

 

Wata majiya ta cikin garin, ta shaida cewa, harin ya afku ne a lokacin sallar asuba da misalin karfe 5:30 na safe, inda ‘yan bindigar suka afkawa masallacin, suka kewaye shi, sannan suka tattara masallatan zuwa daji.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
  • Iran Ta Bayyana Abubuwan Da Bata Amince Da Su Ba A Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar OIC A Birnin Doha
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Kungiyar Human Rights Watch; Isra’ila Ta Kashe ‘Yan Jarida Fiye Da 30 A Kasar Yemen Ne Da Gangan  
  • Kungiyar Kare Hakkokin Bil’Adama Ta Siriya Ta Bankado Karin Fararen Hula Da Aka Kashe A Rikicin Suweida
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar