Shugaban kasar Guinea-Bissau a ya yi wata ganawa da shugaban kasar Rasha
Published: 28th, February 2025 GMT
Shugaban Rasha Vladimir Putin da Shugaban Guinea-Bissau Umaro Sissoco Embalo sun tattauna a fadar Kremlin, yayin da ‘yan adawar Guinea-Bissau suka sha alwashin gurgunta kasar gabanin zabe.
Shugaban kasar Rasha Vladimir Putin da shugaban kasar Guinea-Bissau Umaro Sissoco Embalo, sun yi shawarwari a fadar Kremlin, a wani sabon salo na yunkurin da Moscow ke yi na kulla huldar tattalin arziki da tsaro da kasashen yammacin da tsakiyar Afirka.
Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya habarta cewa, hamshakin attajirin nan na Rasha Oleg Deripaska ya halarci tattaunawar da shugabannin biyu suka yi.
Kafofin yada labarai sun ambato wani minista a Guinea-Bissau, ya ce, Kamfanin aluminium na Rasha Rusal yana sha’awar gina layin dogo da tashar jiragen ruwa a kasar, da kuma binciken ma’adanai na bauxite.”
A wani labarin kuma, ‘yan adawa a kasar Guinea-Bissau sun lashi takobin kawo cikas ga harkokin rayuwa a kasar dake yammacin Afirka a yau Alhamis, sakamakon takaddamar da ta kunno kai dangane da wa’adin mulkin shugaba Umaro Sissoco Embalo na shekaru biyar zai kare.
Shugabannin ‘yan adawa sun ce a cewar Reuters, wa’adin Embalo zai kare ranar Alhamis, yayin da kotun kolin shari’a a Guinea-Bissau ta yanke hukuncin cewa wa’adin ta ya kare a ranar 4 ga Satumba.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Shugaban kasar
এছাড়াও পড়ুন:
Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba
Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya ce sojojin kasar Iran ba za su sararawa gwamnatin Isra’ila ba.
Jagoran ya bayyana hakan ne a wani sakon bidiyo ga al’ummar Iran ranar Juma’a biyo bayan hare-haren wuce gona da iri da Isra’ila ta yi kan kasar wanda ya kashe fararen hula, masana kimiyya da kwamandojin soji.
Ayatullah Khamenei ya kara da cewa gwamnatin Isra’ila ba za ta kubuta daga wannan aika-aika ba, yana mai tabbatar wa al’ummar Iran cewa ba za a yi sakaci kan hakan ba.
Jagoran ya jaddada cewa muguwar gwamnatin sahyoniya ta tafka babban kuskure, sannan kuma shelanta yaki ne kan Iran.
Ayatullah Khamenei ya ci gaba da cewa: dukkanin jami’an kasar Iran da bangarori daban-daban na siyasa da kuma al’ummar Iran suna da ra’ayi daya dangane da wajabcin daukar wani mataki mai karfi wajen tunkarar gwamnatin sahyoniya ta ‘yan ta’adda.
Jagoran ya kara da cewa, bai kamata gwamnatin Isra’ila ta yi tunanin cewa ta ci bulus ba, kuma komi ya wuce.