HausaTv:
2025-07-31@17:39:35 GMT

Aljeriya Ta Yi Watsi Da Barazanar Faransa

Published: 28th, February 2025 GMT

Kasar Aljeriya ta yi watsi da barazanar da kuma wa’adin da kasar faransa ta gindaya ma ta na cewa za ta soke yarjejeniyar da bangarorin biyu suka cimma ta shekarar 1968 wacce ta ba Aljeriya matsayi na musamman.

A wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen kasar Aljeriya ta fitar ta ce “A cikin ci gaba da takun tsakar dake wakana (…) Aljeriya ba ta dauki wani mataki ba, kuma ta bar bangaren Faransa da ta matakin da ya dace.

Ita dai Faransa ta yi barazana a ranar Laraba cewa za ta binciki yarjejeniyoyin da ke saukaka yanayin zama, shige da fice da kuma aiki ga ‘yan Aljeriya, dangane da koma bayan da ake samu na tashe-tashen hankula sakamakon wani hari da aka kai a Mulhouse.

Firaministan faransa, François Bayou ya ce kin karbar ‘yan kasar Aljeriya da aka aka kora daga Faransa ba abu ne da ba za a amince da shi ba, wanda a saboda haka ya baiwa Algiers wa’adin makonni 6 domin nuna aniyar ta na yin hadin gwiwa sosai a kan batutuwan da suka shafi bakin haure, inda ya yi barazanar duba yarjejeniyar 1968 dake tsakanin kasashen biyu.

Kasashen faransa da Aljeriya sun shiga tsakun tsaka matuka a baya baya nan musamman kan batun yankin yammacin sahara na ‘yan Polisario da Aljeriya ke goyan baya, wanda faransa ta amince da ikon shi ga kasar Morocco.

Ko a makon nan majalisar al’ummar Aljeriya, kwatankwacin majalisar dattijai ta kasar, ta sanar da cewa ta “dakatar da hulda da majalisar dattawan Faransa, domin nuna adawa da ziyarar da shugabanta Gérard Larcher ya kai a ranakun Litinin da Talata a yankin yammacin Sahara.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tallafin matar Tinubu na N1bn ga ’yan gudun hijirar Binuwai ya bar baya da kura

Da alama tallafin da matar Shugaban Kasa, Sanata Remi Tinubu ta ba wadanda hare-haren jihar Binuwai ya raba da muhallansu na Naira biliyan daya ya bar baya da kura.

Kwana daya da bayar da tallafin, ’yan gudun hijirar sun fito suna zanga-zangar yunwa, amma kakakin hukumar bayar da agaji ta jihar (SEMA), Terna Ager, ya ce musu kudin ba na sayen abinci ba ne.

Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya

Aminiya ta rawaito yadda Sanata Remi a ranar Talata ta ziyarci jihar inda ta mika wa Gwamnan Jihar, Hyacinth Alia tallafin kudin, a madadin ’yan gudun hijirar.

To sai dai kwana daya bayan hakan, sai wasu daga cikin ’yan gudun hijirar suka fantsama a kan tituna suna zanga-zangar yunwa da zargin masu kula da sansanin da gallaza musu tun da suka tare a can.

Mutanen dai sun tare babbar hanyar Makurdi zuwa Lafiya suna rera wakoki irin su “Gida muke so mu koma,” “Yunwa ta dame mu” da kuma “Matanmu na rasa ’ya’yansu suna yin bari”.

Daya daga cikin matan mai suna Rebecca Awuse, ta shaida wa ’yan jarida cewa, “Yunwa ta ishe mu. Ba mu da abinci, ba muhalli, ba magani sannan ba kulawar lafiya. ’Ya’yanmu na mutuwa da yunwa. Mata da yawa sun yi bari saboda yanayin da suke ciki sannan a kasa muke kwana.

Sai dai da yake mayar da martini, Terna Ager, ya yi zargin cewa akwai wata boyayyar manufar siyasa a zanga-zangar.

A cewarsa, “Babu dalilin da zai sa su yi wannan zanga-zangar sam. Wadanda ke sansanin Yelwata wani lokacin sukan koma sansanin Makurdi an fi samun tallafin abinci a can.

“Tallafin da matar Shugaban Kasa ta bayar na sake tusgunar da su ne ba wain a sayen abinci a raba musu ba ne. Kuma hakan ma yana daukar lokaci.

“Na yi imanin suna zanga-zangar ce saboda suna tunanin za a debi kudin kawai a raba musu, amma ba haka ba ne dalili,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza
  • Tallafin matar Tinubu na N1bn ga ’yan gudun hijirar Binuwai ya bar baya da kura
  • Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa
  • Birtaniya Ta Yi Barazanar Amincewa Da Kasar Falasdinu A Watan Satumba Idan Yanayin Gaza Bai Canza Ba
  • Faransa Ta Bayyana Wuce Gona Da Irin ‘Yan Sahayoniyya Kan Falasdinawa Da Ayyukan Ta’addanci
  • Za mu halasta kafa ƙasar Falasɗinu muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba — Birtaniya
  • Muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba za mu amince da kafa ƙasar Falasɗinu — Birtaniya
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
  • Kasar Faransa Ta Yi Allah Wadai Da Harin Ta’addancin Da Aka Kai Birnin Zahedan Na Kasar Iran
  • Pezeshkiya: Iran A Shirye Take Don Mu’amala Amma Bazata Bar Hakkinta Ba