Leadership News Hausa:
2025-05-01@04:47:29 GMT

Sin Za Ta Ci Gaba Da Tabbatar Da Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya

Published: 27th, February 2025 GMT

Sin Za Ta Ci Gaba Da Tabbatar Da Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian ya bayyana a yau ranar 27 ga wannan wata cewa, kasar Sin za ta ci gaba da maida batun samun bunkasuwa a matsayin batu mafi muhimmanci a cikin ajendar kasa da kasa, da bin tunanin raya al’umma mai kyakkyawar makoma ga dukkan bil Adama, da zama babbar kasa mai ba da muhimmiyar gudummawa a duniya, don tabbatar da bunkasar tattalin arzikin duniya yadda ya kamata.

Lin Jian ya bayyana cewa, kasar Sin ta kiyaye sa kaimi ga bunkasa tattalin arzikin duniya. A matsayin kasa ta biyu mafi ci gaban tattalin arziki a duniya, kasar Sin ta ba da gudummawar kashi 30 cikin dari ga bunkasuwar duniya, kana ita ce muhimmiyar abokiya ta cinikayya ta kasashe da yankuna fiye da 150, da ta kiyaye zama kasa ta farko ta cinikin kaya na duniya, da kasa ta biyu da ke shigar da kayayyaki a kasuwannin duniya, kasar Sin ta zama muhimmiyar kasa da ta samar da kayayyaki da sayar da su a duniya.

Lin Jian ya kara da cewa, kasar Sin ta yi kira ga bunkasa tattalin arzikin duniya bisa tsarin bai daya, da tsaya tsayin daka kan manufar cin gajiyar bunkasar tattalin arziki tare da sauran kasashen duniya cikin adalci. Kasar Sin ta kiyaye bude kofa ga kasashen waje, da samar da yanayin yin kasuwanci mai kyau, da rage jerin sunayen kamfannonin da aka kayyade, don kara samar da kyakkyawar dama ga kamfanonin kasa da kasa. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kasar Sin ta

এছাড়াও পড়ুন:

Wang Yi: Neman Sulhu Da Ja Da Baya Riba Ne Ga Masu Son Cin Zali

Ministan harkokin wajen kasar Brazil Mauro Vieira ne ya jagoranci wannan taro, inda bangarori daban daban suka tattaunawa kan yadda kasashen BRICS za su karfafa zaman lafiya da tsaron duniya. (Mai Fassara: Maryam Yang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yanayin Rudani Na Tsawon Kwanaki 100 Kashedi Ne Ga Amurka
  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030
  • Wang Yi: Neman Sulhu Da Ja Da Baya Riba Ne Ga Masu Son Cin Zali
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Shugaban Putin Na Rasha Ya Bada Sanarwan Tsagaita Wuta Da Ukraine Na Sa’o’ii 72
  • Shin Amurka Na Iya Komawa Kan Kadaminta A Matsayin Cibiyar Masana’antun Duniya?
  • Mutanen da talauci ya yi wa katutu zai ƙaru a Nijeriya — Bankin Duniya
  • Sin Za Ta Aiwatar Da Matakan Daidaita Samar Da Guraben Ayyukan Yi Da Raya Tattalin Arziki
  • Uganda Ta Sanar Da Kawo Karshen Ebola Da Ta Barke A Kasar