Hukumar bunƙasa ƙere-ƙere ta ƙasa (NASENI) ta bayyana cewa an kusa kammala aikin ƙera jirgin sama mai saukar ungulu na farko da aka yi a Nijeriya, kuma nan ba da jimawa ba za a fara gwajin tashinsa. Wannan ci gaba na daga cikin yunƙurin ƙasar wajen bunƙasa fasahar masana’antu da rage dogaro da kayayyakin da ake shigowa da su daga ƙasashen waje.

Manajan Ayyuka na Cibiyar Bunƙasa Jiragen Sama ta NASENI, Injiniya Kareem Aduagba, ya bayyana cewa aikin yana kan hanya, inda ake amfani da dabaru na zamani don haɗa jirgin saman mai suna “Nigerian Chopper.” Ya ce hukumar ba wai tana ƙirƙiro wata sabuwar fasaha ba ne, sai dai tana inganta shirye-shiryen da aka fara tun farko, wanda ya haɗa da jirgin sama mai saukar ungulu da kuma jiragen sama marasa matuƙi (UAVs).

Dambarwar Shirin Tinubu Na Yi Wa Dokar Haraji Kwaskwarima… NASENI Ta Dukufa Kere-kere Domin Kawo Saukin Rayuwa A Nijeriya –Khalil

Injiniya Kareem ya bayyana cewa hukumar ta samo wasu sassa na jirgin sama daga ƙasashen da suka ci gaba a tsarin “Semi Knock Down” (SKD) da “Complete Knock Down” (CKD), tare da amfani da ilimin kimiyya da injiniyanci wajen haɗa su da inganta su. Ya jaddada cewa NASENI tana da himma wajen bunƙasa fasahar cikin gida domin rage dogaro da ƙasashen waje da kuma ƙarfafa masana’antu a ƙasar.

A ƙarshe, ya tabbatar da cewa gwajin tashin jirgin saman zai fara nan ba da daɗewa ba, yayin da ake kammala ƙarin cikakkun matakai na fasaha. Wannan aiki na daga cikin shirin gwamnati na ƙarfafa ƙere-ƙere da fasaha a Nijeriya don inganta harkokin sufurin sama na cikin gida.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Microsoft ya ƙwace shafukan wasu kamfanoni 340 a Najeriya

Kamfanin Microsoft ya sanar da ƙwace shafukan yanar gizo na wasu kamfanoni 340 a Najeriya bayan samunsu da laifin sarrafa fasahohin kamfanin ba bisa ƙa’ida ba, musamman satar bayanan mutane.

Sanarwar da Microsoft ya fitar ta ce matakin ya biyo bayan wani umarni da wata kotu a Amurka ta bayar tun a farkon wannan wata, wadda ta bai wa kamfanin damar ɗaukar matakin ladabtarwa ga waɗanda ke amfani da fasaharsa ba tare da izini ba.

An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe

Steven Masada, mataimakin shugaban sashen lauyoyi na Microsoft da ke kula da laifukan intanet, ya bayyana cewa waɗannan kamfanoni sun ɗauki bayanan abokan hulɗarsu sama da 5,000, inda suka yi amfani da shafukan kutse domin samun bayanan sirri.

A cewarsa, ɗaya daga cikin shafukan da suka fi haddasa damuwa shi ne wani da ake kira Raccoon0356, wanda ke da mabiya fiye da 850 a manhajar Telegram. Wannan shafi ne ke bai wa wasu damar samun kayan aikin kutse don shigar bayanan sirri na Microsoft da wasu hukumomi.

Microsoft ya bayyyana Joshua Ogundipe, mazaunin Najeriya a matsayin wanda ke jagorantar wannan shafi da ke kan manhajar Telegram, kuma bai bayar da amsa a saƙon da aka aike masa ba, don ya kare kanshi game da ayyukan da kamfanin ya ce yana aikatawa.

Kamfanin na Microsoft ya ce ya gano yadda Joshua ya jima tare da ƙwarewa wajen satar bayanan mutane, inda a tsakanin 12 zuwa 28 ga watan Fabrairun wannan shekara, ya yi kutse a shafukan hukumomi sama da 2,300, mafi yawansu na Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • Microsoft ya ƙwace shafukan wasu kamfanoni 340 a Najeriya
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaidai Dake Kasar Yamen
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya