Bankin Raya Afirka ( AFDB) Ya Bayyana Kasashen Da Tattalin Arzikinsu Yake Bunkasa Da Sauri A Cikin Nahiyar
Published: 27th, February 2025 GMT
Bankin Raya Afirka ya sanar da wasu kasashe 10 da ya ce, su ne tattalin arzikinsu yake bunkasa da sauri a cikin nahiyar, tare da yin hashashen cewa gabashin Afirka zai zama sama da sauran yankunan nahiyar a cigaba.
Ana hasashen cewa a cikin rabin kasashen nahiyar za a sami habakar jumillar kudaden shiga ( GDP) daga 4.
A cikin yankin yammacin Afirka kuwa, an tsinkayo cewa tattalin arzikinsu zai tashi daga 4.1% a 2024,zuwa 4.6% a 2025, kuma kasashe irin su Togo, Benin, Cote De Voire, da Gambiya za su sami bunkasa mai karfi.
A Arewacin Afirka kuwa jumillar kudaden shiga ( GDP) zai tashi daga 2.7% a 2024, zuwa 4.2 a 2026.
Kasar Sudan Ta Kudu ce ake hashshen cewa za ta zama zakara a fadin nahiyar ta Afirka wajen bunkasar jumillar kudaden shiga da kaso 34.4%,saboda sake dawowar hako man fetur da kuma fitar da shi zuwa kasuwannin duniya.
Ita kuma Senegal tattalin arzikin nata zai bunkasa ne da kaso 8.9% saboda man fetur, iskar Gas, muhimman cibiyoyi da kuma noma da kiwo.
Kasashen jamhuriyar Nijar, Djibouti, Togo Habasha da Benin da Coye De Voire za su samun bunkasa da kaso 6.3.6.9.% saboda zuba hannun jari a cibiyoyi masu muhimmani da gina su.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Hukumar Kula da Da’ar Ma’aikata Za Ta Fara Daukar Bayanai Ta Yanar Gizo
Hukumar kula da da’ar ma’aikata ta sanar da cewa, a halin yanzu ana iya bayyana kadarorin ma’aikatan ta hanyar yanar gizo, wani mataki da aka tsara domin saukaka aikin da kuma kara yin lissafi.
Daraktan ofishin na jihar Jigawa Abubakar Bello ne ya bayyana haka a lokacin da ya ziyarci shugaban ma’aikatan jihar Alhaji Muhammad K. Dagaceri a ofishin sa.
Abubakar Bello ya jaddada cewa sabon shirin na da nufin rage dinbin aikin dake gaban ma’aiakata da kuma saukaka tantance kadarorin domin yaki da cin hanci da rashawa a cikin tsarin.
“Mun sauya dabara zuwa rajista ta yanar gizo don bayyana kadarorin, muna ba wa mutane damar kammala aikin daga gidajensu. Duk da haka, muna neman goyon bayan ku don tabbatar da cewa an sanar da jami’an gwamnati tare da karfafa gwiwar su bi wannan sabon tsari,” in ji shi.
Da yake mayar da jawabi, shugaban ma’aikata na jiha Alhaji Muhammad K. Dagaceri, ya yi alkawarin wayar da kan jami’an gwamnati cikin tsanaki game da muhimmancin bayyana kadarorin su, kamar yadda hukumar da’ar ma’aikata ta ba su umarni.
Ya tunatar da cewa rashin yin biyayya ga kundin tsarin mulkin kasa ne.
Dagaceri ya bada tabbacin bada goyon baya da hadin kai domin cimma burin da ake so na wannan shiri.
USMAN MZ