Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-09-18@00:55:20 GMT

Sarkin Moroko Ya Buƙaci Yan Kasar Kada Su Yi Layya A Bana

Published: 27th, February 2025 GMT

Sarkin Moroko Ya Buƙaci Yan Kasar Kada Su Yi Layya A Bana

Sarkin Moroko, Mohammed na shida, ya buƙaci ƴan ƙasar su kaurace wa layya a bana wanda al’ummar Musulmi masu hali ke yanka dabobbi, musamman rago a matsayin nuna godiya ga Allah bisa rayawa da ni’imomin da ya yi wa bayinsa.Sarkin ya ce sanarwar tasa na da alaƙa da karancin raguna da ake fuskanta a ƙasar sakamakon fari.

A watan Yunin bana ake sa ran gudanar da bikin sallar Layya. Layya ibada ce da al’ummar musulmi ke yi a cikin watan Zhul Hajji.

A bikin Sallar layyar ana yanka dabobbi da suka danganci raguna da awaki ta hanyar zubar da jini a kuma raba naman a matsayn kyauta da sadaka don neman kusanci ga ubanjigi.

Sai dai Sarki Mohammed na moroko ya umarci al’ummarsa su jingine batun layya a bana saboda fari ya haifar da karancin dabobbi a kasar.An samu raguwar raguna da kashi 40 cikin 100 a cikin shekaru 10 a ƙasar saboda fari.

Farashin nama yayi tashin gwaran zabi, kuma a kullum ake shigo da dubban raguna kasar daga Australia

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Layya Maroko

এছাড়াও পড়ুন:

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za A Kada Kuri’ar Raba Gardama Akan Sabon Tsarin Mulki A Kasar Guinea
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
  • Espania Ta Soke Cinikin Makamai Na EUR Miliyon 700 Da HKI Saboda Kissan Kiyashi A Gaza
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
  • KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin
  • Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya