HausaTv:
2025-06-15@18:22:00 GMT

Isra’ila Ta Kai Hare-hare A Kudancin Syria

Published: 26th, February 2025 GMT

Jiragen yakin Isra’ila sun kai hare-hare da dama a kan wasu sansanonin soji a kudancin kasar Siriya, ciki har da wasu yankunan da ke wajen Damascus babban birnin kasar da kuma lardin Deraa da ke kudancin kasar.

Hare-haren dai ya biyo bayan kiran da firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya yi na karbe yankin kudancin Siriya baki daya.

Jaridar Yedioth Ahronoth ta Isra’ila ta kuma bayar da rahoton cewa, Tel Aviv ta fara aiwatar da wani shiri na “shiga kudancin Syria.

Ministan tsaron Isra’ila, Israel Katz, ya ce jiragen yakin Isra’ila sun kai hare-hare a kudancin Syria a daren Talata, yana mai cewa harin wani bangare ne na sabuwar manufar Isra’ila ta “kawar da ayyukan soji a kudancin Syria.”

A cikin wata sanarwa da Katz ya fitar, ya ce harin wani bangare ne na manufar da firaminista Benjamin Netanyahu ya sanar a ranar Litinin, na “kawar da ayyukan soji kudancin Syria.”

Ya kara da cewa, za a tarwatsa duk wani yunkuri na dakarun sabuwar gwamnatin Syria da kungiyoyin ‘yan tawaye na kafa kansu a kudancin Syria.

A daya bangaren kuma, kafofin yada labaran kasar Syria sun rawaito cewa jiragen yakin Isra’ila sun kai hare-hare da dama a kudancin kasar ta Syria, yayin da sojojin kasa suka kutsa kai tsakanin Daraa da Quneitra dake kudancin kasar.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: a kudancin Syria kudancin kasar kai hare hare

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila

Dakarun kare juyin juya halin Musulunci (IRGC) sun kaddamar da wani sabon harin makamai masu linzami da jirage marasa matuka kan Isra’ila a cikin daren jiya Asabar, biyo bayan matakin farko na harin ramuwar gayya na kan harin Isra’ila na ranar Juma’a.

Jim kadan bayan harba makamai masu linzami da jirage marasa matuka, sashen hulda da jama’a na IRGC ya ba da sanarwar kaddamar da wani sabon shiri na manyan makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka.

Sanarwar ta yi nuni da cewa, sashen kula da sararin samaniya na IRGC ya fara wannan sabon mataki na aikin a matsayin mayar da martani kai tsaye ga sabbin ta’addancin gwamnatin sahyoniyawan.

Babban abin da aka fi mayar da hankali kan wannan sabon farmakin na ‘Operation True Promise III’ an bayar da rahoton cewa, birnin Haifa mai tashar jiragen ruwa ya kunshi muhimman wuraren soji da masana’antu na gwamnatin.

Hare-haren sun shafi wasu muhimman cibiyoyin soji da masana’antu na Isra’ila, da suka hada da matatun mai da na wutar lantarki a Haifa, inda aka ce gobara ta tashi a sanadiyar haka.

Daya daga cikin faifan bidiyon ya nuna wata gagarumar gobara da ta tashi a matatar mai ta Haifa bisa tasirin da manyan makamai masu linzami na Iran suka yi, wanda ya haskaka sararin samaniyar yankunan da aka mamaye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Cilla Makamai Kan HKI Da Rana A Karon Farko A Yau Lahadi
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Ba’a Rufe Kofar Diblomasiyya Ba, Matukar HKI Ta Dakatar Da Kaiwa Kasar HKI
  • Sojojin Kasar Iran Sun Ce Bazasu Dakatar Da Yaki ba Har Zuwa Samun Nasara A kan HKI
  • Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
  • Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
  • Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila
  • Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bude Kofofin Jahannama Ga Yahudawan Sahayoniyya
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • IRGC : Iran ta kai hare hare wurare a kalla 150 a Isra’ila