Tattalin arzikin Nijeriya ya haɓaka da kashi 3.84 — NBS
Published: 25th, February 2025 GMT
Hukumar Ƙididdiga ta Nijeriya NBS ta ce tattalin arzikin ƙasar ya haɓaka da kaso 3.84 cikin 100 a zango na 4 na shekarar 2024.
A cewar rahoton da hukumar NBS ta fitar a yau Talata, bunƙasar ta ɗara kaso 3.46 da aka samu a zango na 3 na 2024.
An naɗa Obasanjo mai shiga tsakani a rikicin Kongo Manoman tumatir na tafka asara saboda faɗuwar farashiAlƙaluman game da zango na 4 na shekarar 2024 sun kuma ɗara kaso 3.
“Ɓangaren ayyuka ne kan gaba a bunƙasar ta zango na 4 na 2024, wanda ya ƙaru da kaso 5.37 cikin 100 tare da ba da gudunmawar kaso 57.38 cikin 100 na jimillar tattalin arzikin,” a cewar NBS.
A jimillar ƙididdigar shekarar ta 2024, tattalin arzikin Nijeriya ya haɓaka ne da kashi 3.40 idan aka kwatanta da kashi 2.74 a 2023.
Sai dai duk da haka, haɓakar ba ta cimma alƙawarin da Shugaba Bola Tinubu ya ɗauka na haɓaka tattalin arziƙin ƙasar da kashi 6 ba a shekarar ta 2024.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Nijeriya Tattalin Arziki tattalin arzikin
এছাড়াও পড়ুন:
Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
Shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar amfani da ƙarfin soji kan Najeriya matuƙar gwamnatin ƙasar ba ta dakatar da kisan da ’yan ta’adda masu iƙirarin jihadi ke yi wa Kiristoci ba.
A yammacin jiya Asabar ne Trump ya umarci Ma’aikatar Yaƙin Amurka ta Pentagon da ta soma tsara yadda za a kai hari Nijeriya bayan da ya yi zargin cewa ana yi wa Kiristoci kisan gilla a ƙasar.
Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Truth Social, Trump ya ce Amurka a shirye ta ke ta aike da sojoji da manyan makamai cikin Najeriya don bai wa Kiristocin kariya.
Barazanar shugaban na Amurka na zuwa ne kwana guda bayan ya yi iƙirarin cewa an kashe Kiristoci aƙalla 3,100 a Nijeriya ba tare da ya bayyana takamaimai inda ya samu waɗannan alƙaluma ba.
“Muddin gwamnatin Nijeriya ta ci gaba da bari ana kashe Kiristoci, Amurka za ta dakatar da dukkan tallafin da take bai wa Nijeriya nan-take, kuma mai yiwuwa za ta shiga wannan ƙasƙantacciyar ƙasar, cike da ƙarfin gwiwa domin kawar da ’yan ta’adda masu kaifin kishin Musulunci waɗanda ke yin wannan ta’asa,” in ji Trump.