Aminiya:
2025-09-18@00:56:54 GMT

Za a kafa ƙarin makarantu a Zariya — Abbas Tajudeen

Published: 23rd, February 2025 GMT

Shugaban Majalisar Wakilai, Dokta Abbas Tajudeen ya ce Kasafin Kuɗin Nijeriya na baɗi zai ba da damar kafa ƙarin makarantu na matakin Tarayya a mazaɓarsa ta Zariya.

Shugaban majalisar ya bayyana haka ne lokacin babban taron shekara-shekara karo na 31 da 32 na ƙungiyar bunkasa ilimi ta Zariya, watau ZEDA da aka gudanar a Zariya.

Mai Pataskum ya buɗe masallacin garin Danga a Yobe An kama mutum biyu kan kisan wata mata saboda maita

Ya bayyana cewa makarantun da ake shirin kafa wa sun haɗa da makarantar firamare da sakandare na yara masu buƙata ta musamman da kwalejin tarayya na koyon aikin noma da kiwo.

Shugaban majalisar ya kuma bayyana fara bada tallafin na musamman ga ɗaliɓin da ya fi kowa kwazo a fannin koyon ilimin kwamfuta da kuma ɗalibin da ya fi kowa nuna hazaƙa a bangaren makarantun sakandare da ke larɗin Zazzau.

Ya bayyana rashin jin daɗi bisa jinkirin da aka samu wajen biyan ɗalibai 2500 kuɗin tallafin karatu da suke lardin Zazzau, yana mai cewa za a ƙara yawan ɗaliban da za su riƙa cin moriya tallafin zuwa 3000 a shekarar 2026.

Shugaban majalisar ya ɗora alhakin jinkirin da aka samu wajen biyan tallafin akan kaddamar da kasafin kuɗin shekarar 2024, inda ya bayyana cewa za a biya kuɗin da zarar al’amura sun daidaita.

Haka kuma, ya ba da sanarwar cewa zai gina wa ƙungiyar ZEDA tare da sanya kayayyaki irin na zamani a ɗakin taro da zai ɗauki kimanin mutane dubu ɗaya.

Shugaban majalisar ya ƙara da cewa kudurin majalisar ne ganin ta bunkasa ilimi a matakin farko da inganta ilimin sakandare da na kimiyya da kawo sauyi a fannonin ƙirƙira.

Ya buƙaci kungiyar ZEDA da ta ɓullo da wani tsari da zai samar da yanayin bai wa malamai horo da shigar da iyaye cikin harkokin tattauna batutuwan da suka shafi ilimi.

Tun farko a jawabinsa na maraba, shugaban kwamitin tsare-tsare na kungiyar ta ZEDA, Dokta Abdul Alimi Bello ya ce kungiyar ta sami gagarumar nasara da ya nuna aniyar ta na samar da ingantaccen ilimi da bunƙasa al’umma.

Ya ce cikin shekaru da dama, ƙungiyar ta kasance jagoran kungiyoyi masu zaman kansu a lardin Zazzau da suke kula da ilimin zamani da bunkasa sana’o’in hannu.

A nasa jawabin, mai martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli ya buƙaci ƙungiyar da ta yi amfani da kuɗaɗen shigar ta wajen tabbatar da samar da kyakkyawan sauyi a ɓangaren ilimi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: makarantu Zariya Shugaban majalisar ya

এছাড়াও পড়ুন:

Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya

Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II ya koka bisa yawan bashin da Najeriya ke ciyowa da kuma yadda gwamnati ke facaka da kuɗaɗen.

Sarkin wanda tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN) ne, ya kuma bayyana cewa cire tallafin man fetur da Gwamnatin Tarayya ta yi shi ne mafi alheri, yana  mai cewa da Gwamnatin ba ta cire tallafin mai ba, da Najeriya ta daɗe da tsiyacewa.

“Adawata a ɓangaren shan man ne, saboda muna ba da aikin yi ga matatun mai a Turai. Muna ba da aikin ga masu tace ɗanyen man,” in ji Sarki Sanusi.

Da yake jawabi a Taron Adabi na Duniya na Kano (KAPFEST) da aka gudanar a Kano ranar Asabar, masanin tattalin arzikin ya bayyana cewa ɗabi’ar yawan cin bashin Najeriya za ta yi mummunar illa ga tattalin arzikin ƙasar na tsawon lokaci.

Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki Gidauniyar Misilli ta mayar da yara 150 makaranta a Gombe

Masanin tattalin arzikin ya bayyana damuwa musamman kan yadda gwamnati ke kashe kuɗaɗen da ta ciyo bashin.

Zuwa ƙarshen watan Maris, yawan bashin da ake bin Najeriya ya haura Naira tiriliyan 150.

A yayin taron wanda cibiyar Poetic Wednesdays Initiative (PWI), ta shirya, Sarki Sanusi II ya ce, ya ce, “Ina muke kai wannan tulin bashin da muke ciyowa a ƙasar nan?

“Zan yi farin cikin ganin an yi amfani da kuɗaɗen a fannin ilmantar da matasanmu, saboda su ne za su biya. Amma bai kamata mu yi ciyo bashi muna lafta wa tattalin arzikin ƙasa ba tare da zuba jari a fannin ilmantar da waɗanda su ne za su biya bashin ba.

“Nan da shekara 20 za mu faɗa a matsala a dalikin cin bashi. Dole a zuba jari a fannin inganta rayuwarsu domin samar da abubuwa.”

Ya bayyana cewa Najeriya ba ta yi sa’ar shugabanni nagari ba a tsawon lokaci, yana mai cewa yawancin shugabannin ƙasar ragwage ne masu yawan kawo uzuri.

Sarki Sanusi II ya bayyana kyakkyawan shugabanci a matsayin muhimmin abin da zai ceto Najeriya daga halin da take ciki, wanda ya kira na rashin sa’a.

Da yake sukar yanayin koma-bayan Najeriya alhali wasu ƙasashe sun yi gaba ta fannin kimiyya da fasaha da ci-gaban zamani, Sarki Sanusi II ya buƙaci matsala da su tashi domin karɓar ragamar shugabancin ƙasar, yana mai jaddada cewa hakan abu mai yiwuwa ne idan matasan suka jajirce.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UNICEF Ya Ba Da Tallafin Kayayyakin Aiki Ga Cibiyoyin Lafiya A Kirikasamma
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Runduwar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai
  • Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya