Za a kafa ƙarin makarantu a Zariya — Abbas Tajudeen
Published: 23rd, February 2025 GMT
Shugaban Majalisar Wakilai, Dokta Abbas Tajudeen ya ce Kasafin Kuɗin Nijeriya na baɗi zai ba da damar kafa ƙarin makarantu na matakin Tarayya a mazaɓarsa ta Zariya.
Shugaban majalisar ya bayyana haka ne lokacin babban taron shekara-shekara karo na 31 da 32 na ƙungiyar bunkasa ilimi ta Zariya, watau ZEDA da aka gudanar a Zariya.
Ya bayyana cewa makarantun da ake shirin kafa wa sun haɗa da makarantar firamare da sakandare na yara masu buƙata ta musamman da kwalejin tarayya na koyon aikin noma da kiwo.
Shugaban majalisar ya kuma bayyana fara bada tallafin na musamman ga ɗaliɓin da ya fi kowa kwazo a fannin koyon ilimin kwamfuta da kuma ɗalibin da ya fi kowa nuna hazaƙa a bangaren makarantun sakandare da ke larɗin Zazzau.
Ya bayyana rashin jin daɗi bisa jinkirin da aka samu wajen biyan ɗalibai 2500 kuɗin tallafin karatu da suke lardin Zazzau, yana mai cewa za a ƙara yawan ɗaliban da za su riƙa cin moriya tallafin zuwa 3000 a shekarar 2026.
Shugaban majalisar ya ɗora alhakin jinkirin da aka samu wajen biyan tallafin akan kaddamar da kasafin kuɗin shekarar 2024, inda ya bayyana cewa za a biya kuɗin da zarar al’amura sun daidaita.
Haka kuma, ya ba da sanarwar cewa zai gina wa ƙungiyar ZEDA tare da sanya kayayyaki irin na zamani a ɗakin taro da zai ɗauki kimanin mutane dubu ɗaya.
Shugaban majalisar ya ƙara da cewa kudurin majalisar ne ganin ta bunkasa ilimi a matakin farko da inganta ilimin sakandare da na kimiyya da kawo sauyi a fannonin ƙirƙira.
Ya buƙaci kungiyar ZEDA da ta ɓullo da wani tsari da zai samar da yanayin bai wa malamai horo da shigar da iyaye cikin harkokin tattauna batutuwan da suka shafi ilimi.
Tun farko a jawabinsa na maraba, shugaban kwamitin tsare-tsare na kungiyar ta ZEDA, Dokta Abdul Alimi Bello ya ce kungiyar ta sami gagarumar nasara da ya nuna aniyar ta na samar da ingantaccen ilimi da bunƙasa al’umma.
Ya ce cikin shekaru da dama, ƙungiyar ta kasance jagoran kungiyoyi masu zaman kansu a lardin Zazzau da suke kula da ilimin zamani da bunkasa sana’o’in hannu.
A nasa jawabin, mai martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli ya buƙaci ƙungiyar da ta yi amfani da kuɗaɗen shigar ta wajen tabbatar da samar da kyakkyawan sauyi a ɓangaren ilimi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: makarantu Zariya Shugaban majalisar ya
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Ivory Coast Ya Bayyana Shirinsa Na Sake Tsayawa Takarar Shugabanci Karo Na Hudu
Shugaban kasar Ivory Coast Alhassan Outtara ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugabancin kasar a karo na 4 wanda za a gudanar a watan Oktoba mai zuwa.
Za a yi manyan zabukan kasar ta Ivory Coast ne dai a ranar 25 ga watan na Oktoba mai zuwa.
Shi dai Alassan Outtara an sake zabarsa shugaban kasa karo na uku a 2020, alhali tun a baya ya sanar da cewa zai sauka daga kan mukamin nashi.
Outtara ya zama shugaban kasar ta Ivory Coast a karon farko a 2010 a kasar da ita ce mafi girma wajen fitar da Coco a duniya.
Kamfanin dillancin labarun “Reuters’ ya amabto Ottata yana cewa: “Tsarin mulkin kasarmu ya ba ni damar in sake yin hidima a wani jikon, kuma inda da cikakkiyar lafiyar da za ta sa in yi hakan.”
Haka nan kuma ya ce; Ina sake tsaywa takara saboda kasarmu tana fuskantar kalubale mai girma a fagagen tattalin arziki da tsaro da ba a tsaba fuskantar irinsa ba a baya.
Gabanin zamansa shugaban kasa, Outtara ya kasance kwararre a fagen tattalin arziki wanda ya yi karatunsa a kasar Amurka. Daga cikin ayyukan da ya yi da akwai gwamnan Bankin yammacin Afirka, sannan kuma mataimakin shugaban Asusun Bayar da Lamuni Na Duniya ( IMF).
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu July 30, 2025 MDD Zata Aiwatar Da Hanyar Warware Rikicin Falasdinawa Da Yahudawan Sahayoniyya July 30, 2025 Birtaniya Ta Yi Barazanar Amincewa Da Kasar Falasdinu A Watan Satumba Idan Yanayin Gaza Bai Canza Ba July 30, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Lod Da Ke Jaffa Da Makami Mai Linzami July 30, 2025 Faransa Ta Bayyana Wuce Gona Da Irin ‘Yan Sahayoniyya Kan Falasdinawa Da Ayyukan Ta’addanci July 30, 2025 Jagora: Iran Ta Bayyana Karfinta Da Jajircewarta A Yakin Kwanaki 12 Ga Duniya July 29, 2025 Mutum daya Yayi Shahada 4 Sun Ji Rauna Sanadiyar Hare-Haren HKI A Lebanon July 29, 2025 EU Tace Zata Dakatar Da HKI Daga Cibiyar Bincikenta Saboda Gaza July 29, 2025 Ma’aikatar Leken Asirin JMI Ta Ce Ta Gano Shirin Kashe Manyan Mutane 35 a kasar July 29, 2025 Najeriya: Likitoci a Lagas Sun Shiga Yajin Aiki July 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci