Aminiya:
2025-09-18@00:52:22 GMT

An ƙwace miliyoyin daloli, gidajen da ke da alaƙa da Emefiele

Published: 21st, February 2025 GMT

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Legas ta bayar da umarnin a ƙwace Dala miliyan 4.7 da Naira miliyan 830 da wasu kadarori da dama da ke da alaƙa da tsohon Gwamnan babban bankin Najeriya (CBN) Godwin Emefiele.

Da yake yanke hukunci a ranar Juma’a, Mai shari’a Yellim Bogoro, wanda a baya ya yi watsi da buƙatar kama Emefiele, ya amince da buƙatar hukumar yaƙi da yi wa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa ta EFCC, wadda lauya Bilkisu Buhari-Bala ta wakilta.

’Yan sanda sun daƙile satar mutane, sun kama wasu 3 a Borno Ba ni da hannu a kisan Dele Giwa — Janar Babangida

Kuɗaɗen da a halin yanzu gwamnatin tarayya ta ƙwace, sun kasance a cikin asusun bankunan: First Bank, Titan Bank da Zenith Bank da wasu mutane da hukumomi suke kula da su da suka haɗa da: Omoile Anita Joy, kamfanin Deep Blue Energy Serɓice Limited, kamfanin Exactquote Bureau De Change Ltd, Kamfanin Lipam Investment Services Limited, kamfanin Tatler Services Limited, kamfanin Rosajul Global Resources Ltd, da kamfanin TIL Communication Nigeria Ltd.

Kaddarorin da aka ƙwace na wucin gadi sun haɗa da:  Ɗakuna 94 na wani bene mai hawa 11 da ake ginawa a 2 Otunba Elegushi 2nd Aɓenue, Ikoyi, Legas; da AM Plaza, ofisoshi mai hawa 11 a ginin Otunba Adedoyin Crescent, Lekki Peninsula Scheme 1, a Legas; da Imore Industrial Park 1 a Esa Street, Imoore Land, a Ƙaramar Hukumar Amuwo Odofin a Legas; Mitrewood and Tatler Warehouse kusa da Elemoro, Village Owolomi, Ibeju-Lekki LGA, Lagos; da kadarori biyu da aka saya daga kamfanin Chevron Nigeria, da ke cikin rukunin gidaje na Estate Lakes a Lekki da ke Legas.

Mai shari’a Bogoro ya bayyana cewa, duk waɗannan kadarori da kuɗaɗe ne na wasu ayyuka da suka saɓawa ƙa’ida, waɗanda gwamnatin tarayyar Najeriya za ta iya kwace  su.

Alƙalin ya ce: “Na ga cewa ayyukan waɗanda ake ƙara a nan ba halastattu be ne. Me zai sa su samu matsalar dala nan take, Godwin Emefiele ya bar CBN a matsayin gwamnan Banki kuma an kasa biyan albashi?

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Matakin hana malaman da ba su da rajista hawa mumbari a Neja yana ci gaba da yamutsa hazo a ciki da wajen jihar.

Yayin da wasu suke ganin wannan mataki bai dace ba, wasu kuwa gani suke faduwa ta zo daidai da zama, wato matakin ya zo a daidai lokacin da ake bukata.

NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau Uku

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kan tanadin Dokar Kasa game da wannan batu.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kammala Ziyarar Yini 3 A Ma’aikatar Kananan Hukumomin Jihar
  • Microsoft ya ƙwace shafukan wasu kamfanoni 340 a Najeriya
  • Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
  • Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta