Aminiya:
2025-08-01@19:07:33 GMT

’Yan sanda sun daƙile satar mutane, sun kama wasu 3 a Borno

Published: 21st, February 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Borno, ta daƙile wani yunƙuri da ’yan bindiga suka yi na sace wani mutum a Sabon Garin Lassa da ke Ƙaramar Hukumar Askira Uba.

Rundunar ta kuma cafke wasu mutum uku tare da ƙwato wata bindiga ƙirar gida a hannunsu.

Babban mai kai wa Bello Turji makamai ya shiga hannu NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Ba Za Mu Sauke Farashin Burodi Ba —’Yan kasuwa

Majiyoyin tsaro sun shaida wa Zagazola Makama cewa, lamarin ya faru ne a ranar 20 ga watan Fabrairu da misalin karfe 1 na dare.

Wasu ’yan bindiga huɗu suka kai hari gidan Mohammed Abubakar, mazaunin Sabon Gari Lassa, da nufin sace shi.

“Wanda suka yi niyyar sacewa ya yi ƙoƙarin kare kansa da adda, lamarin da ya tilasta wa maharan tserewa ba tare da sun cimma burinsu ba”, in ji majiyar.

Bayan haka, Abubakar, ya gaggauta kiran ’yan sanda, inda tare da haɗin gwiwar ’yan banga, jami’an tsaro suka bi sahun ’yan bindigar zuwa maɓoyarsu.

A sakamakon haka, rundunar ‘yan sanda ta cafke mutum uku da ake zargi, dukkaninsu mazauna ƙauyen Gajali da ke Ƙaramar Hukumar Askira Uba.

“Haka kuma an ƙwato wata bindiga da aka ƙera a gida daga hannun waɗanda ake zargin,” in ji majiyar.

Rundunar ’yan sandan jihar, ta yaba da yadda jami’an tsaro suka mayar da martani cikin gaggawa, tare da yin kira ga al’umma da su kasance masu lura da duk wani abu da ba su saba gani ba.

Ta kuma buƙaci su gaggauta kai rahoto ga jami’an tsaro domin ɗaukar mataki a kan lokaci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Yan Sanda Askira Uba hari Satar Mutane

এছাড়াও পড়ুন:

Gaza: Mutane Da Dama Sun Yi Shahada A Yau Wasu Kuma Sun Jikkata

Haramtacciyar kasar Isra’ila ta ci gaba da kai hare-hare a zirin Gaza a yau Juma’a, inda ta kai munanan hare-hare kan yankunan fararen hula da sansanonin ‘yan gudun hijira.

Wadannan hare-haren sun yi sanadiyar mutuwar mutane da dama da kuma jikkatar wasu a fadin yankin, lamarin da ke kara zurfafa damuwar da ake da ita game da mawuyacin da al’ummar yankin suke ciki.

Kamfanin Nasser Medical Complex ya bayar da rahoton a wannan  Juma’a cewa, wani harin da jiragen saman Isra’ila suka kai kan tantunan da mutane suke fakewa a yankin Al-Mawasi da ke yammacin Khan Younis, ya kashe mutane hudu tare da jikkata wasu da dama.

A wani harin  na daban a kusa da Morag a kudancin birnin Gaza, an kashe mutane biyu tare da jikkata wasu sama da 70 da ke neman agaji.

A wani harin da aka kai a yankin Ard al-Fara da ke kudancin Khan Younis, an kashe fararen hula uku da suka hada da yaro daya da mace daya a lokacin da aka kai hari kan tantunan ‘yan gudun hijira.

A yankin Deir al-Balah da ke tsakiyar Gaza kuwa Isra’ila ta kashe mutane hudu tare da jikkata wasu.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Haaretz: Sojojin Isra’ila 7 ne suka kashe kansu a watan Yuli August 1, 2025 Kungiyar AU Ta Yi Watsi Da Kafa Gwamnatin Adawa Da Kungiyar RSF Ta Yi A Sudan August 1, 2025 Shugaban Kasar Iran Zai Ziyarci Pakistan A Gobe Asabar August 1, 2025 Habasha Ta Kaddamar Da Shirin Shuka Bishiyoyi Miliyan 700 A Rana Daya August 1, 2025 Sayyid Abdulmalik Husi: Taimakon Da Ake Jefawa Gaza Ta Sama Yaudara Ce August 1, 2025 Amurka Ta Kakabawa Jami’an Gwamnatin Falasdinawa Takunkuman Hana Shiga Amurka July 31, 2025 Ministan Harkokin Wajen Siriya Yana Rasha Don Bude Sabon Shafi Tsakaninsu July 31, 2025 Kananan Yan Wasan Dabben Gargajiya Na Iran Sun Zama Zakara A Gasar Wannan Shekara July 31, 2025 Canada Zata Amince Da Samuwar Kasar Falasdinu A Taron MDD July 31, 2025  Shugaban Kasar Lebanon Aun Ya Ce Mun Aike Wa  Amurka Sakwanni Akan Dakatar Da Hare-haren HKI July 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An ceto mutum uku da aka yi garkuwa da su a Kebbi
  • Iran ta yi watsi da zargin gwamnatocin turai na yunkurin kashe wasu mutane a kasashensu
  • Gaza: Mutane Da Dama Sun Yi Shahada A Yau Wasu Kuma Sun Jikkata
  • ‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu 
  • ZAMFARA: APC Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Dauki Don Matsalar Tsaro Na Kara Tsananta
  • Hare-hare: ’Yan bindiga sun raba mutum 5,000 da muhallansu a Katsina
  • Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno
  • Sojoji sun daƙile hari, sun kashe mayaƙan Boko Haram 9 a Borno
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga