Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-06-15@11:30:33 GMT

Matasan Jihar Jigawa Sun Karrama Gwamna Umar Namadi

Published: 20th, February 2025 GMT

Matasan Jihar Jigawa Sun Karrama Gwamna Umar Namadi

Gwamnatin Jihar Jigawa ta dauki matasa fiye da 6,000 aiki a fannoni daban-daban a fadin jihar, a kokarinta na ganin ta inganta rayuwarsu.

A saboda haka ne ma matasan da aka dauka aikin suka karrama Gwamnan Jihar, Malam Umar Namadi, bisa kokarinsa na samar da ayyukan yi da bunkasa tattalin arzikin al’ummar jihar.

Wakilinmu Usman Mohammed Zaria ya ruwaito cewa, taron karramawar, wanda aka gudanar a gidan Gwamnati dake Dutse Babban Birnin Jihar, ya hada da wadanda suka ci gajiyar shirye-shiryen gwamnati da suka hada da  J-Teach, da  J-Agro, da  J-Health, da  J-Millionaires, da sabbin likitocin da aka dauka aiki a bangaren lafiya.

A yayin taron, kowanne rukuni ya mika lambar yabo ga Gwamna Umar Namadi don nuna godiya bisa kokarinsa na ci gaban matasa tare da sharbar romon dimokradiyya.

A jawabin sa, Gwamna Umar Namadi ya nuna matukar farin cikinsa da wannan karramawar da matasan suka yi masa.

Yana mai cewar wannan girmamawar ba tasa ce kadai ba,  ta daukacin al’ummar Jihar Jigawa ce gaba daya ba shi kadai ba.

A don haka, ya yaba wa matasan bisa jajircewarsu wajen kafa kyakkyawar rayuwa nan gaba, da kuma taimakawa ci gaban al’umma.

Malam Umar Namadi, ya yi nuni da cewar, matasan Jigawa sun nuna kwarewa da kishin kasa wajen tabbatar da ci gaban jihar.

Yana mai cewar, shakka babu, da irin wannan himma da kwazon matasa, jihar za ta ci gaba da samun ci gaba a fannoni da dama.

Sai dai kuma, Namadi ya bukaci matasan da su ci gaba da kokari wajen bunkasa jihar, yana mai jaddada cewar ci gaban Jigawa na hannun al’ummarta.

Ya kuma tabbatar da kudirin gwamnatinsa na kara samar da damarmaki ga matasa, ta hanyar daukar aiki, da kuma bunkasa tattalin arziki, domin tabbatar da kyakkyawar makoma ga jihar.

Taron ya samu halartar Kakakin Majalisar dokokin Jihar, Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin da Sakataren Gwamnatin, Malam Bala Ibrahim da kwamishinoni da sauran jami’an gwamnatin Jihar.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Umar Namadi

এছাড়াও পড়ুন:

Cikakken Jerin Sunaye: Tinubu Ya Karrama ‘Yan Nijeriya 102 Don Bukin Ranar Dimokuradiyya Ta 2025

 

Sai dai kuma shugaba Tinubu ya yi amfani da wannan damar wajen yi wa shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio, da kakakin majalisar wakilai Tajudeen Abbas ado da lambar yabo ta GCON, yayin da mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau Jibrin da mataimakin kakakin majalisar, Benjamin Kalu, da lambar yabo ta CFR.

 

Ga cikakken jerin sunayen sabbin mutane 67 da aka karrama da lambar yabon, kamar yadda fadar shugaban kasa ta fitar:

 

Grand Commander of the Order of the Niger (GCON).

 

Shehu Musa Yar’Adua

Rt Hon Tajudeen Abbas

Senator Godswill Akpabio

Wole Soyinka

 

Commander of the Order of the Niger (CON)

Ghali Umar Na’Abba

Salisu Buhari

Umaru Dikko

Uche Chukwumerije

Bala Mohammed Gwagwarwa

Aisha Yesufu

Innocent Chukwuma

Tony Nnadi

Olisa Agbakoba

Nuhu Ribadu

Hafsat Abiola-Costello

Tunde Bakare

Kabiru Yusuf

Jibrin Ibrahim

Clement Nwankwo

Alao Aka Bashorun

Alhaja Sawaba Gambo

Barrister Felix Moria

Bayo Onanuga

Bishop Mathew Hassan Kukah

Chief Frank Kokori

Dare Babarinsa

Dr John Yuma Sen

Dr Alex Ibru

Dr Amos Ayingba

Dr Beko Ransome Kuti

Dr Edwin Madunagu

Dr Kayode Shonoiki

Dr Nurudeen Olowpopo

Femi Falana, SAN

Fredrick Fasehun

Governor Uba Sani

Ken Saro Wiwa

Ladin Mitee

Mobolaji Akinyemi

Olawale Osun

Prof Bayo Williams

Prof Humphrey Nwosu

Prof Julius Ihonvbere

Prof Olayinji Dare

Prof Segun Gbadegesin

Prof Shafideen Amuwo

Prof Festus Iyayi

Rear Admiral Ndubuisi Kanu

Senator Ayo Fasanmu

Senator Polycarp Nwite

Senator Shehu Sani

Tokumbo Afikuyomi

Tunji Alausa

 

Officer of the Order of the Niger (OON)

Abdul Oroh

Ayo Obe

Bagauda Kaltho

Bamidele Aturu

Baribor Bera

Barinem Kiobel

Chima Ubani

Daniel Gboko

Dapo Olorunyomi

Emma Ezeazu

Felix Nuate

John Kpuine

Kunle Ajibade

Labaran Maku

Luke Aghanenu

Nick Dazang

Nordu Eawo

Nosa Igiebor

Paul Levera

Sam Amuka Pemu

Saturday Dobee

Seye Kehinde

 

Commander Of The Federal Republic

Alhaji Balarabe Musa

Chief Bola Ige

Kudirat Abiola

Pa Alfred Rewane

Pa Reuben Fasaranti

Rt. Hon Benjamin Okezie Kalu

Sen Abu Ibrahim

Sen Ame Ebute

Sen Jibrjn Ibrahim Barau

Member of the Federal Republic (MFR)

Ibijoke Faborode

Seun Onigbinde

Samson Itodo

Ezenwa Nwagwu

Kemi Okenyodo

Akin Akingbulu

Raymond Duke Tenebe

Oby Nwankwo

Abiola Akiyode-Afolabi

Ariyo-Dare Atoye

Ndidi Nwuneli

Auwal Musa Rafsanjani

Y.Z. Ya’u

Jaiye Gaskia

Jaye Gaskia

Issa Aremu

Hamzat Lawal

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa
  • Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya
  • Cikakken Jerin Sunaye: Tinubu Ya Karrama ‘Yan Nijeriya 102 Don Bukin Ranar Dimokuradiyya Ta 2025
  • Fahimtar Sabon Tunani: Raya Kimiyya Da Fasaha Da Dogaro Da Karfi Na Kashin Kai Sun Ingiza Ci Gaban Kasar Sin 
  • Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara
  • An hana hawa babur da daddare a fadin jihar Gombe