Matasan Jihar Jigawa Sun Karrama Gwamna Umar Namadi
Published: 20th, February 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Jigawa ta dauki matasa fiye da 6,000 aiki a fannoni daban-daban a fadin jihar, a kokarinta na ganin ta inganta rayuwarsu.
A saboda haka ne ma matasan da aka dauka aikin suka karrama Gwamnan Jihar, Malam Umar Namadi, bisa kokarinsa na samar da ayyukan yi da bunkasa tattalin arzikin al’ummar jihar.
Wakilinmu Usman Mohammed Zaria ya ruwaito cewa, taron karramawar, wanda aka gudanar a gidan Gwamnati dake Dutse Babban Birnin Jihar, ya hada da wadanda suka ci gajiyar shirye-shiryen gwamnati da suka hada da J-Teach, da J-Agro, da J-Health, da J-Millionaires, da sabbin likitocin da aka dauka aiki a bangaren lafiya.
A yayin taron, kowanne rukuni ya mika lambar yabo ga Gwamna Umar Namadi don nuna godiya bisa kokarinsa na ci gaban matasa tare da sharbar romon dimokradiyya.
A jawabin sa, Gwamna Umar Namadi ya nuna matukar farin cikinsa da wannan karramawar da matasan suka yi masa.
Yana mai cewar wannan girmamawar ba tasa ce kadai ba, ta daukacin al’ummar Jihar Jigawa ce gaba daya ba shi kadai ba.
A don haka, ya yaba wa matasan bisa jajircewarsu wajen kafa kyakkyawar rayuwa nan gaba, da kuma taimakawa ci gaban al’umma.
Malam Umar Namadi, ya yi nuni da cewar, matasan Jigawa sun nuna kwarewa da kishin kasa wajen tabbatar da ci gaban jihar.
Yana mai cewar, shakka babu, da irin wannan himma da kwazon matasa, jihar za ta ci gaba da samun ci gaba a fannoni da dama.
Sai dai kuma, Namadi ya bukaci matasan da su ci gaba da kokari wajen bunkasa jihar, yana mai jaddada cewar ci gaban Jigawa na hannun al’ummarta.
Ya kuma tabbatar da kudirin gwamnatinsa na kara samar da damarmaki ga matasa, ta hanyar daukar aiki, da kuma bunkasa tattalin arziki, domin tabbatar da kyakkyawar makoma ga jihar.
Taron ya samu halartar Kakakin Majalisar dokokin Jihar, Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin da Sakataren Gwamnatin, Malam Bala Ibrahim da kwamishinoni da sauran jami’an gwamnatin Jihar.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Umar Namadi
এছাড়াও পড়ুন:
Cikakken Jerin Sunaye: Tinubu Ya Karrama ‘Yan Nijeriya 102 Don Bukin Ranar Dimokuradiyya Ta 2025
Sai dai kuma shugaba Tinubu ya yi amfani da wannan damar wajen yi wa shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio, da kakakin majalisar wakilai Tajudeen Abbas ado da lambar yabo ta GCON, yayin da mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau Jibrin da mataimakin kakakin majalisar, Benjamin Kalu, da lambar yabo ta CFR.
Ga cikakken jerin sunayen sabbin mutane 67 da aka karrama da lambar yabon, kamar yadda fadar shugaban kasa ta fitar:
Grand Commander of the Order of the Niger (GCON).
Shehu Musa Yar’Adua
Rt Hon Tajudeen Abbas
Senator Godswill Akpabio
Wole Soyinka
Commander of the Order of the Niger (CON)
Ghali Umar Na’Abba
Salisu Buhari
Umaru Dikko
Uche Chukwumerije
Bala Mohammed Gwagwarwa
Aisha Yesufu
Innocent Chukwuma
Tony Nnadi
Olisa Agbakoba
Nuhu Ribadu
Hafsat Abiola-Costello
Tunde Bakare
Kabiru Yusuf
Jibrin Ibrahim
Clement Nwankwo
Alao Aka Bashorun
Alhaja Sawaba Gambo
Barrister Felix Moria
Bayo Onanuga
Bishop Mathew Hassan Kukah
Chief Frank Kokori
Dare Babarinsa
Dr John Yuma Sen
Dr Alex Ibru
Dr Amos Ayingba
Dr Beko Ransome Kuti
Dr Edwin Madunagu
Dr Kayode Shonoiki
Dr Nurudeen Olowpopo
Femi Falana, SAN
Fredrick Fasehun
Governor Uba Sani
Ken Saro Wiwa
Ladin Mitee
Mobolaji Akinyemi
Olawale Osun
Prof Bayo Williams
Prof Humphrey Nwosu
Prof Julius Ihonvbere
Prof Olayinji Dare
Prof Segun Gbadegesin
Prof Shafideen Amuwo
Prof Festus Iyayi
Rear Admiral Ndubuisi Kanu
Senator Ayo Fasanmu
Senator Polycarp Nwite
Senator Shehu Sani
Tokumbo Afikuyomi
Tunji Alausa
Officer of the Order of the Niger (OON)
Abdul Oroh
Ayo Obe
Bagauda Kaltho
Bamidele Aturu
Baribor Bera
Barinem Kiobel
Chima Ubani
Daniel Gboko
Dapo Olorunyomi
Emma Ezeazu
Felix Nuate
John Kpuine
Kunle Ajibade
Labaran Maku
Luke Aghanenu
Nick Dazang
Nordu Eawo
Nosa Igiebor
Paul Levera
Sam Amuka Pemu
Saturday Dobee
Seye Kehinde
Commander Of The Federal Republic
Alhaji Balarabe Musa
Chief Bola Ige
Kudirat Abiola
Pa Alfred Rewane
Pa Reuben Fasaranti
Rt. Hon Benjamin Okezie Kalu
Sen Abu Ibrahim
Sen Ame Ebute
Sen Jibrjn Ibrahim Barau
Member of the Federal Republic (MFR)
Ibijoke Faborode
Seun Onigbinde
Samson Itodo
Ezenwa Nwagwu
Kemi Okenyodo
Akin Akingbulu
Raymond Duke Tenebe
Oby Nwankwo
Abiola Akiyode-Afolabi
Ariyo-Dare Atoye
Ndidi Nwuneli
Auwal Musa Rafsanjani
Y.Z. Ya’u
Jaiye Gaskia
Jaye Gaskia
Issa Aremu
Hamzat Lawal
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp