An Rantsar Da Sabbin Shugabannin Kungiyar Manyan Sakatarorin Jihar Zamfara
Published: 19th, February 2025 GMT
Kungiyar manyan sakatarorin ma’aikatun jihar Zamfara(ZASPEF) ta sha alwashin ci gaba da bayar da shawarwari don inganta iyyuka da sha’anin mulki.
Zababben shugaba Malam Yakubu Sani Haidara ne ya bayyana hakan a lokacin kaddamar da su a matsayin sabbin shugabannin kungiyar a Gusau.
Yakubu Sani Haidara ya bayyana cewa, yayin da ma’aikatan gwamnati ke ci gaba da bunkasa, za su ci gaba da bayar da shawarwarin ci gaba da gudanar da shirye-shirye na inganta karfin harkokin mulki.
Shugaban ya bayyana cewa, wannan yunkurin zai sa a fi amfani da shawarwarin manyan Sakatarorin wajen tsara manufofi da aiwatar da su.
Sani Haidara ya kuma ce a matsayinsu na manyan masu gudanar da mulki, ya ba da tabbacin goyon bayansu ga gwamnati mai ci ta Gwamna Dauda Lawal.
A jawabinsa na bude taron, shugaban riko na kungiyar mai barin gado Muhammad Abubakar, ya ce sun yi aiki tukuru wajen ganin sun samar da fahimtar juna a tsakanin manyan sakatarorin da ya kai ga samar da wani gagarumin dandali da ke samar da hadin kai, da bayar da shawarwari da kuma kwarewa a aiki.
Ya bukaci sabbin shugabannin da su ci gaba da inganta ayyukan yi a jihar Zamfara.
Shi ma da yake jawabi, shugaban taron kuma shugaban hukumar ma’aikatan jihar Zamfara Alhaji Aliyu Muhammad Tukur, ya yi kira ga sabbin shugabannin kungiyar da su yi aiki tukuru domin tabbatar da amincewar da aka yi musu ta hanyar sadaukar da kai da kuma aiki da gaskiya.
Sabbin shugabannin kungiyar ta Zamfara State Permanent Secretaries’ Forum (ZASPEF) sun hada da Yakubu Sani Haidara a matsayin shugaba, da Dr. Barira Ibrahim Bagobiri mataimakiyar shugaba, da Shehu Baraya Gusau a matsayin ma’ajin kudin,
da Bashir Usman Salihu jami’in hulda da jama’a.
Yayin da sauran su ne Yazid Attahiru mai binciken kudi, da
Musa Garba Bukkuyum mai bada shawara kan harkokin shari’a,
da Garba Aliyu Gayari, a matsayin Sakatare.
Aminu Dalhatu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Manyan Sakatarorin Gwamnati Zamfara shugabannin kungiyar Sani Haidara
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Ci gaba da killace Gaza da kuma kashe mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, laifi ne da ba a taba yin irinsa ba a tarihin dan Adam
A wata tattaunawa ta wayar tarho da takwaransa na Masar Badar Abdel Ati a yammacin jiya Lahadin da ta gabata, Araqchi ya bayyana ci gaba da killace yankin Gaza da rashin abinci da magunguna, tare da kashe mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, a matsayin wani laifi da ba a taba ganin irinsa ba a tarihin dan Adam. Ya dauki Amurka da sauran masu goyon bayan ‘yan sahayoniyya a matsayin masu hannu a kisan kiyashi da laifukan yaki da ake aikatawa a Gaza.
Ministan harkokin wajen na Iran ya jaddada wajibcin tunkarar muggan manufofin yahudawan sahayoniyya na tilastawa al’ummar Gaza da yammacin kogin Jordan yin hijira daga muhallinsu, yana mai bayyana halin ko in kula da kasashen duniya suke nun awa kan wadannan laifuka a matsayin abin mamaki da damuwa.
Araghchi ya kuma yi wa takwaransa na Masar bayani kan ci gaban tattaunawar Iran da Amurka kan Shirin makamashin nukiliya na zaman lafiya da ake takaddama a kai tsawon shekaru.