Kungiyar manyan sakatarorin ma’aikatun jihar Zamfara(ZASPEF) ta sha alwashin ci gaba da bayar da shawarwari don inganta iyyuka da sha’anin mulki.

Zababben shugaba Malam Yakubu Sani Haidara ne ya bayyana hakan a lokacin kaddamar da su a matsayin sabbin shugabannin kungiyar a Gusau.

Yakubu Sani Haidara ya bayyana cewa, yayin da ma’aikatan gwamnati ke ci gaba da bunkasa, za su ci gaba da bayar da shawarwarin ci gaba da gudanar da shirye-shirye na inganta karfin harkokin mulki.

Shugaban ya bayyana cewa, wannan yunkurin zai sa a fi amfani da shawarwarin manyan  Sakatarorin wajen tsara manufofi da aiwatar da su.

Sani Haidara ya kuma ce a matsayinsu na manyan masu gudanar da mulki, ya ba da tabbacin goyon bayansu ga gwamnati mai ci ta Gwamna Dauda Lawal.

A jawabinsa na bude taron, shugaban riko na kungiyar mai barin gado Muhammad Abubakar, ya ce sun yi aiki tukuru wajen ganin sun samar da fahimtar juna a tsakanin manyan sakatarorin da ya kai ga samar da wani gagarumin dandali da ke samar da hadin kai, da bayar da shawarwari da kuma kwarewa a aiki.

Ya bukaci sabbin shugabannin da su ci gaba da inganta ayyukan yi a jihar Zamfara.

Shi ma da yake jawabi, shugaban taron kuma shugaban hukumar ma’aikatan jihar Zamfara Alhaji Aliyu Muhammad Tukur, ya yi kira ga sabbin shugabannin kungiyar da su yi aiki tukuru domin tabbatar da amincewar da aka yi musu ta hanyar sadaukar da kai da kuma aiki da gaskiya.

Sabbin shugabannin kungiyar ta Zamfara State Permanent Secretaries’ Forum (ZASPEF) sun hada da Yakubu Sani Haidara a matsayin shugaba, da Dr. Barira Ibrahim Bagobiri mataimakiyar shugaba, da Shehu Baraya Gusau a matsayin ma’ajin kudin,
da Bashir Usman Salihu jami’in hulda da jama’a.

Yayin da sauran su ne Yazid Attahiru mai binciken kudi, da
Musa Garba Bukkuyum mai bada shawara kan harkokin shari’a,
da Garba Aliyu Gayari, a matsayin Sakatare.

Aminu Dalhatu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Manyan Sakatarorin Gwamnati Zamfara shugabannin kungiyar Sani Haidara

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi

A cewarsa, dukkanin takardar neman kirkirar sabon masarauta ko sarki ko gunduma dole ne a aike zuwa addireshin gwamnan jihar ta hannun babbar sakatariyar ma’aikatar kananan hukumomi da kula da masarautu na jihar.

Kazalika, ya ce dole ne masu nema su gabatar da takaitaccen tarihin al’ummar da suke nema wa masarauta ko sarki ko gudunmawa tare da tarihin masarautar ko sarki ko gundumar da ke yankin da suke neman fita daga ciki.

Sanarwar ta kuma nemi a sanya dukkanin wani muhimmin bayanin da aka san zai iya taimakawa wajen la’akari da bukatar masu nema.

Har ila yau, sanarwar ta ce dole ne a takardar neman a samu sahihin sanya hannun hakimi, sarakunam kauye, da shugabannin al’umma tare da tabbacin wannan neman ta fito ne daga al’ummar wannan yankin da ake nema mata masarauta ko sarki ko gunduma.

Sanarwar ta kara da cewa duk al’ummomin da ke son kirkirar sabbin masarautu, sarakuna, ko gundumomi su na da dama kuma su na da ‘yancin gabatar da bukatar neman.

Gidado ya jaddada cewa shirin na daya daga cikin kudirin gwamnati na bunkasa gudanar da harkokin kananan hukumomi, da kiyaye al’adu, da karfafa cibiyoyin gargajiya a matsayin muhimman ginshikan zaman lafiya, hadin kai, da ci gaba masu ma’ana.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
  • Jagoran Juyin Musulunci Na Iran Ya Nada Sabbin Kwamandojin Soja Da Dakarun Kare Juyin Musulunci
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi
  • Harin Isra’ila a kan Iran ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zama dar-dar
  • Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi
  • Nijeriya Ce Ta 3 A Manyan Kasashe Masu Karfin Masana’antu 10 Na Afirka
  • Leroy Sane ya koma Galatasaray
  • Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki