An Rantsar Da Sabbin Shugabannin Kungiyar Manyan Sakatarorin Jihar Zamfara
Published: 19th, February 2025 GMT
Kungiyar manyan sakatarorin ma’aikatun jihar Zamfara(ZASPEF) ta sha alwashin ci gaba da bayar da shawarwari don inganta iyyuka da sha’anin mulki.
Zababben shugaba Malam Yakubu Sani Haidara ne ya bayyana hakan a lokacin kaddamar da su a matsayin sabbin shugabannin kungiyar a Gusau.
Yakubu Sani Haidara ya bayyana cewa, yayin da ma’aikatan gwamnati ke ci gaba da bunkasa, za su ci gaba da bayar da shawarwarin ci gaba da gudanar da shirye-shirye na inganta karfin harkokin mulki.
Shugaban ya bayyana cewa, wannan yunkurin zai sa a fi amfani da shawarwarin manyan Sakatarorin wajen tsara manufofi da aiwatar da su.
Sani Haidara ya kuma ce a matsayinsu na manyan masu gudanar da mulki, ya ba da tabbacin goyon bayansu ga gwamnati mai ci ta Gwamna Dauda Lawal.
A jawabinsa na bude taron, shugaban riko na kungiyar mai barin gado Muhammad Abubakar, ya ce sun yi aiki tukuru wajen ganin sun samar da fahimtar juna a tsakanin manyan sakatarorin da ya kai ga samar da wani gagarumin dandali da ke samar da hadin kai, da bayar da shawarwari da kuma kwarewa a aiki.
Ya bukaci sabbin shugabannin da su ci gaba da inganta ayyukan yi a jihar Zamfara.
Shi ma da yake jawabi, shugaban taron kuma shugaban hukumar ma’aikatan jihar Zamfara Alhaji Aliyu Muhammad Tukur, ya yi kira ga sabbin shugabannin kungiyar da su yi aiki tukuru domin tabbatar da amincewar da aka yi musu ta hanyar sadaukar da kai da kuma aiki da gaskiya.
Sabbin shugabannin kungiyar ta Zamfara State Permanent Secretaries’ Forum (ZASPEF) sun hada da Yakubu Sani Haidara a matsayin shugaba, da Dr. Barira Ibrahim Bagobiri mataimakiyar shugaba, da Shehu Baraya Gusau a matsayin ma’ajin kudin,
da Bashir Usman Salihu jami’in hulda da jama’a.
Yayin da sauran su ne Yazid Attahiru mai binciken kudi, da
Musa Garba Bukkuyum mai bada shawara kan harkokin shari’a,
da Garba Aliyu Gayari, a matsayin Sakatare.
Aminu Dalhatu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Manyan Sakatarorin Gwamnati Zamfara shugabannin kungiyar Sani Haidara
এছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikatar Leken Asirin JMI Ta Ce Ta Gano Shirin Kashe Manyan Mutane 35 a kasar
Ma’aikatar leken asiri na JMI ta bada sanarwan cewa ta gano shirin makiya na kashe manya-manyan Jami’an gwamnati har 35 a kasar kafin yakin da suka dorawa kasar.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto majiyar ma’aikatar na fadar haka, ta kuma kara da cewa a cikin yakin kwanaki 12 sun yi kokarin kashe many-manyan Jami’an gwamnati har 35 a cikin yakin. Da kuma wasu 13 watanni kafin yakin, amma saboda matakan da ma’aikatar ta dauka hakan bai faru ba.
Labarin ya kara da cewa, hukumar a tsaye take kan makirce-makircen makiya, sannan kuma tana daukar matakan da suka dace don hana kutsawar su a cikin kasar da kuma cutar da shuwagabanni da kuma mtanen gari.
A wani bangare kuma hukumar ta bayyana cewa tana ayyukan leken asiri kan HKI da kuma shirye-shiyenta nag aba. Tana samun ma’aikata a cikin sojoji da jami’an tsaro na HKI. Sannan ta kara da cewa ma’aikatansu kadanne yahudawan suka kama.
Majiyar ta kara da cewa ta sami bayanan sirri kan shirye-shrye masu muhimmanci na HKI daga ciki har da bayani dangane da shirinta na makaman Nukliya.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Najeriya: Likitoci a Lagas Sun Shiga Yajin Aiki July 29, 2025 Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai July 29, 2025 Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu July 29, 2025 Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta July 29, 2025 Manjo Janar Musawi: Ko Kadan Ba Mu Yarda Da Amurka Ba July 29, 2025 Araqchi: Iran Zata Mayar Da Martanin Da Ba Zai Yiwu A Boye Ba Kan Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kanta July 29, 2025 Kasar Iran Ta Musanta Yin Katsalandan A Tattaunawar Neman Tsagaita Bude Wuta A Gaza July 29, 2025 Rasha Ta Mayar Da Martani Ga Shugaban Amurka Kan Gindaya Wa’adin Kawo Karshen Yakin Ukraine July 29, 2025 Kasar Faransa Ta Yi Allah Wadai Da Harin Ta’addancin Da Aka Kai Birnin Zahedan Na Kasar Iran July 29, 2025 Wakilin Gidan Talabijin Na Al-Alam Ya Bayyana Yadda Shi Da Iyalansa Suka Rayu Kwanaki Biyu Babu Abinci A Gaza July 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci