A ranar 17 ga watan Fabrairu, agogon birnin New York ne, aka yi wani zama na musamman na nuna fim din Nezha 2 a hedikwatar Majalisar Dinkin Duniya dake birnin New York na kasar Amurka, wanda hukumar kula da fina-finai ta kasar Sin, da babban rukunin gidajen radiyo da talabijin na kasar Sin wato CMG, da kuma kungiyar masu sha’awar karanta littattafai na kasar Sin dake MDD suka dauki nauyin shiryawa tare.

Fiye da baki 150 da suka hada da mataimakin babban sakataren MDD Xu Haoliang, da jami’an diflomasiyyar kasashen Faransa, Rasha, Girka, Thailand da sauran kasashe a MDD, da ma’aikatan hedikwatar MDD, da ’yan jarida sun halarci bikin nuna fim din.

Xu Haoliang, mataimakin babban sakataren MDD ya bayyana cewa, sakin fim din Nezha 2 a kasashe da yankuna da dama na duniya ya sa kaimi ga mu’amala tsakanin jama’a da al’adu tsakanin kasar Sin da sauran kasashe. Fim din ya hada kasashe da al’adu daban-daban ta hanyar ba da tatsuniyoyi da labaru a cikin al’adun gargajiya na kasar Sin, wanda ya kara samun fahimtar juna tsakanin al’umma. Yadda aka shirya fim din Nezha 2 ya kuma nuna cewa, bunkasuwar fasahar shirya fina-finan cartoon ta kasar Sin ta kai matsayi na duniya. (Mohammed Yahaya)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu

 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya November 1, 2025 Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya November 1, 2025 Daga Birnin Sin Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar
  • Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu
  • IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya
  • Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
  • Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba