An Nuna Nezha 2 A Zama Na Musamman A Hedikwatar MDD Dake Birnin New York
Published: 19th, February 2025 GMT
A ranar 17 ga watan Fabrairu, agogon birnin New York ne, aka yi wani zama na musamman na nuna fim din Nezha 2 a hedikwatar Majalisar Dinkin Duniya dake birnin New York na kasar Amurka, wanda hukumar kula da fina-finai ta kasar Sin, da babban rukunin gidajen radiyo da talabijin na kasar Sin wato CMG, da kuma kungiyar masu sha’awar karanta littattafai na kasar Sin dake MDD suka dauki nauyin shiryawa tare.
Xu Haoliang, mataimakin babban sakataren MDD ya bayyana cewa, sakin fim din Nezha 2 a kasashe da yankuna da dama na duniya ya sa kaimi ga mu’amala tsakanin jama’a da al’adu tsakanin kasar Sin da sauran kasashe. Fim din ya hada kasashe da al’adu daban-daban ta hanyar ba da tatsuniyoyi da labaru a cikin al’adun gargajiya na kasar Sin, wanda ya kara samun fahimtar juna tsakanin al’umma. Yadda aka shirya fim din Nezha 2 ya kuma nuna cewa, bunkasuwar fasahar shirya fina-finan cartoon ta kasar Sin ta kai matsayi na duniya. (Mohammed Yahaya)
এছাড়াও পড়ুন:
Tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa har zuwa baɗi — IMF
Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta hasashen cewa tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa tun daga shekarar nan ta 2025 har zuwa 2026.
IMF ya bayyana sabon hasashen a watan Yulin da muke ciki wanda a ciki ya yi ƙiyasin samun ƙarin bunƙasar tattalin arzikin Nijeriya.
Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasaAsusun ya yi hasashen samun ƙarin bunƙasar tattalin arzikin Nijeriya da kashi 3.4 a 2025, ƙari a kan hasashen kashi 3.0 da ya yi a watan Afrilu.
Haka kuma, IMF ya yi hasashen cewa tattalin arzikin Nijeriya zai samun ƙarin bunƙasa da kashi 3.2 a 2026, saɓanin hasashen kashi 2.7 da ya yi a watan na Afrilu.
Sai dai duk da wannan, wani rahoto IMF ya fitar a watan Yunin bana, ya ce Nijeriya na mataki na 12 a cikin jerin kasashe mafiya talauci a fadin duniya.
IMF ya ce talauci na kara karuwa a cikin kasar da ta dauki shekaru biyu tana kokarin sauya fuskar tattalin arziki, amma kuma take dada fadawa cikin duhu na tattalin arziki.
A cikin kasashe 189 da aka gudanar da bincike a cikinsu, Nijeriyar na a mataki na 178, inda ta zarta kasashe irin su Yemen da Sudan ta Kudu da Kwango da Nijar da Sudan, wadanda kusan dukkaninsu ke fama da rigingimu a halin yanzu.