Yadda Fim Din “Ne Zha 2” Ya Samu Matukar Karbuwa A Duniya Bai Zo Da Mamaki Ba
Published: 18th, February 2025 GMT
Yawan kudin tikitin kallon fim din “Ne Zha 2” na kasar Sin da aka saya ya zarce dala biliyan 16 a daren jiya, abin da ya sa ya shiga sahun fina-finai 9 mafi samun yawan kudin tikitin kallon fim dake sahun gaba a duniya. Dalilin da ya sa fim din samun wannan ci gaba shi ne ingancin abin da ya kunsa.
Labarin da wannan fim ya gabatar ya yi daidai da wasan yanar gizo mai suna “Black Myth: Wukong”, wanda shi ma na kasar Sin ne.
Idan aka duba bangaren fasahar zamani ta wannan fim, za a ga cewa, an kwashe shekaru 5 ana tsara fim din na “Ne Zha 2”, wanda ya kunshi hotuna na musamman kusan 2,000 da wasu abubuwa na musamman masu tasiri a shirin fim sama da 10,000. Matakin da ya nuna cewa, fina-finan Cartoon da Sin ta kirkiro ba kawai sun amfani da fasahar waje ba, har ma a yanzu sun iya zama ma’aunin da za a yi misali da shi.
Ban da wannan kuma, fim din ya bayyana dankon zumuncin iyali da abokai masu nuna zaman tare da zuciya daya, kuma ya nuna yadda mutanen fim din suka yi iyakacin kokarinsu wajen kare garinsu da iyalansu, abin da ya dace da nagartaccen tunanin Bil-Adama na bai daya. Shi ya sa fim din ya zama mai taba zuciyar masu kallo na kasa da kasa. Abin da kuma har ila yau ya nuna cewa, zuciyoyin Bil-Adama a kusa suke da juna, wadda hakan ke iya daidaita mabambantan ra’ayoyin al’adu a tsakanin kasashe daban-daban, da kara mu’amala da cudanyar al’ummun duniya. (Amina Xu)
এছাড়াও পড়ুন:
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
An gudanar da taron tattaunawa na duniya kan kirkire-kirkire da bude kofa da ci gaba na bai daya, jiya Juma’a a birnin Lagos na Nijeriya. Yayin taron wanda babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin CMG da karamin ofishin jakadancin Sin dake Lagos suka shirya, ministan kula da harkokin matasa na Nijeriya Ayodele Olawande da shugaban CMG Shen Haixiong, sun gabatar da jawabai ta kafar bidiyo.
A cewar ministan na Nijeriya, cikin shekaru 5 da suka gabata, dubban matasan kasar sun ci gajiyar tallafin karatu da shirye-shiryen horo da na musaya da Sin ta samar, kuma wannan hadin gwiwa da ake yi a aikace ya kara fahimta da aminci tsakanin kasashen biyu. Ya kara da cewa, a shirye ma’aikatarsa take ta karfafa hadin gwiwa da sassa masu ruwa da tsaki na kasar Sin wajen ci gaba da fadada shirye-shiryen musaya da na hadin gwiwa da suka shafi matasa.
A nasa bangare, Shen Haixiong ya ce a matsayinta na babbar kafar yada labarai dake watsa shirye shiryenta ga sassa daban daban na duniya, tashar talabijin ta CCTV dake karkashin CMG da abokan huldarta, za su yayata shawarar Sin ta jagorantar harkokin duniya da gabatar da tafarkin Sin na zamanantar da kanta da karfinta na kirkire kirkire a sabon zamani ga al’ummar duniya. (Mai fassara: FMM)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA