Yadda Fim Din “Ne Zha 2” Ya Samu Matukar Karbuwa A Duniya Bai Zo Da Mamaki Ba
Published: 18th, February 2025 GMT
Yawan kudin tikitin kallon fim din “Ne Zha 2” na kasar Sin da aka saya ya zarce dala biliyan 16 a daren jiya, abin da ya sa ya shiga sahun fina-finai 9 mafi samun yawan kudin tikitin kallon fim dake sahun gaba a duniya. Dalilin da ya sa fim din samun wannan ci gaba shi ne ingancin abin da ya kunsa.
Labarin da wannan fim ya gabatar ya yi daidai da wasan yanar gizo mai suna “Black Myth: Wukong”, wanda shi ma na kasar Sin ne.
Idan aka duba bangaren fasahar zamani ta wannan fim, za a ga cewa, an kwashe shekaru 5 ana tsara fim din na “Ne Zha 2”, wanda ya kunshi hotuna na musamman kusan 2,000 da wasu abubuwa na musamman masu tasiri a shirin fim sama da 10,000. Matakin da ya nuna cewa, fina-finan Cartoon da Sin ta kirkiro ba kawai sun amfani da fasahar waje ba, har ma a yanzu sun iya zama ma’aunin da za a yi misali da shi.
Ban da wannan kuma, fim din ya bayyana dankon zumuncin iyali da abokai masu nuna zaman tare da zuciya daya, kuma ya nuna yadda mutanen fim din suka yi iyakacin kokarinsu wajen kare garinsu da iyalansu, abin da ya dace da nagartaccen tunanin Bil-Adama na bai daya. Shi ya sa fim din ya zama mai taba zuciyar masu kallo na kasa da kasa. Abin da kuma har ila yau ya nuna cewa, zuciyoyin Bil-Adama a kusa suke da juna, wadda hakan ke iya daidaita mabambantan ra’ayoyin al’adu a tsakanin kasashe daban-daban, da kara mu’amala da cudanyar al’ummun duniya. (Amina Xu)
এছাড়াও পড়ুন:
Adadin Falasdinawan da Isra’ila take kashewa a Gaza yanzu ya haura 60,000
A ci gaba da hare-haren da dakarun Isra’ila ke kai wa a Zirin Gaza, yanzu adadin Falasdinawan da suka kashe ya kai 60,034.
A cewar wasu alkaluma daga Ma’aikatar Lafiya ta Gaza, baya ga wannan, adadin wadanda aka raunata kuma a yanzu sun haura 145,870.
Ma’aikatar ta kuma ce har yanzu ana zargin akwai mutanen kuma da ke karkashin baraguzan gine-ginen da aka rusa, wadanda ba za a iya ciro su daga ciki ba.
Fiye da kaso daya cikin uku na mutanen yankin na shafe kwanaki ba su ci abinci ba, kamar yadda wani rahoton samar da abinci mai lakabin IPC na Majalisar Dinkin Duniya ya tabbatar.
Rahoton ya ce ana samun karin hujjoji da ke nuna ana fama da yunwa da karancin abinci da kuma karuwar mace-mace masu alaka da yunwa a yankin da sama da mutum miliyan biyu da dubu dari daya ke rayuwa a cikinsa.
Hukumomi daban-daban na Majalisar Dinkin Duniya dai sun yi gargadin cewa ana fama da matsananciyar yunwar da aka kirkira da gangan a Gaza, inda a iya wannan watan, rahotanni suka tabbatar da mutuwar mutum 63, dalilin yunwar.
Hukumomin dai sun dora wa Isra’ila duk alhakin matsalolin, kasancewar ita ta yi wa yankin kawanya ta kuma hana a shigar da kayan agaji.
Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya, António Guterres, ya ce: “Abubuwa ne ga su nan a Zahiri, ba a boye suke ba. Falasdinawan da suke Gaza na cikin mawuyacin hali da tsananin bukatar agaji.
“Wannan ba wai gargadi muke yi ba. Gaskiya ce ga ta nan karara. Dole kayan agaji su ci gaba da kwarara. Abinci, ruwan sha, magunguna da man fetur dole su ci gaba da shiga ba tare da kowanne irin tarnaki ba,” in ji Guterres.