Aminiya:
2025-06-15@17:41:05 GMT

Za a binciki INEC kan jinkirin gudanar da zaɓen cike giɓi

Published: 18th, February 2025 GMT

Majalisar Wakilai ta umarci kwamitinta kan harkokin zaɓe da ya binciki Hukumar Zaɓe ta Ƙasa INEC dangane da jinkirin da take yi na gudanar da zaɓen cike giɓin wasu kujerun ’yan majalisar tarayya da na jihohi.

Majalisar a wannan Talatar ta kuma bayyana cewa jazaman ne kwamitin ya gayyaci Hukumar INEC domin ta bayar da dalilai kan tsaikon da aka samu da kuma yadda take ƙoƙarin yi wa tufkar hanci.

Gubar harsashi ta jikkata mutane dama a Zamfara Da wahala City ta yi nasara a gidan Madrid — Guardiola

Aminiya ta ruwaito cewa Majalisar ta buƙaci kwamitin ya sauke wannan nauyi tare da miƙa mata rahoton bincikensa nan da makonni huɗu.

Wannan dai na zuwa ne bayan ƙorafin da wani ɗan majalisar, Jafaru Leko ya gabatar yana mai kafa hujja da Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya wanda ya ɗora wa INEC alhakin gudanar da zaɓe a faɗin ƙasar.

Kazalika, ya naƙalto sassa na 47 da 90 da ke cikin Kundin Tsarin Mulkin wanda ya hukunta assasa majalisun tarayya da na jihohi a matsayin wani rukuni na ’yancin ’yan ƙasa su samu wakilci.

Ya yi ƙorafin cewa tun bayan Zaɓen 2023 da waɗanda suka biyo baya, an samu giɓi a majalisun tarayya da na jihohi saboda wasu dalilai kamar mutuwa, karɓar wasu muƙaman ko ajiye aiki.

Jafara Leko ya ci gaba da ƙorafin cewa Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya ya yi tanadin gudanar da zaɓen cike giɓi cikin tsawon lokacin da bai gaza wata guda ba da samun giɓin.

Ya ƙara da cewa, gudanar da zaɓen wanda alhakinsa ya rataya a wuyan Hukumar INEC shi ne zai tabbatar da wakilcin kowace mazaɓa a ƙasar.

A cewarsa, wannan jinkiri da INEC take ci gaba da yi rashin biyayya ne ga Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya, lamarin da ke cutar da al’umma ko mazaɓar da ba su wakilci a hukumance.

Aminiya ta ruwaito cewa, a halin yanzu akwai kujerun ’yan Majalisar Tarayya bakwai masu giɓi da suka haɗa da na Majalisar Wakilai biyar da kuma biyu a Majalisar Dattawa.

Kujerun da ke da giɓi a Majalisar Wakilan sun haɗa da na jihohin Edo, Oyo, Kaduna, Ogun da Jigawa sai kuma na Majalisar Dattawa da suka ƙunshi Edo da Anambra.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Wakilai Zaɓe Kundin Tsarin Mulkin gudanar da zaɓen a Majalisar

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Oman ta tabbatar da soke tattaunawar Iran da Amurka zagaye na shida
  • Miliyoyin Mutane Sun Gudanar  Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran
  • Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa
  • An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka
  • Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran
  • Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung
  • Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje
  • Mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu — Tinubu
  • Iran ta caccaki kudurin IAEA wanda ta ce yana cike da siyasa