Shugaban kasar Amurka ya bayyana cewa: Fira ministan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ya aikata duk abin yake so

Shugaban Amurka Donald Trump ya yi nuni da wa’adin da ya bayar dangane da yarjejeniyar tsagaita bude wuta da kuma sakin fursunonin, yana mai cewa ya shaidawa fira ministan gwamnatin mamayar Isra’ila  Benjamin Netanyahu ya aika duk abin da yake so.

Trump ya tabo batun mataki na gaba – ana sa ran za a fara tattaunawa nan ba da jimawa kan kashi na biyu na yarjejeniyar – ya ce: “Ya rage ga gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila kan mataki na gaba, tare da tuntubarsa.”

An kuma tambayi Trump ko jinkirin jigilar makamai zuwa haramtacciyar kasar Isra’ila a karkashin Shugaba Biden zai “hana tsagaita bude wuta?,” inda ya amsa da cewa: “Wannan ana kiransa zaman lafiya ta hanyar karfi.

Kalaman na zuwa ne bayan da Netanyahu ya sanar da cewa zai kira taro domin tattaunawa kan mataki na biyu na yarjejeniyar da ya kamata a bude makonni biyu da suka gabata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kassim: Duk Wanda Yake Neman Hizbullah Ta Ajiye Makamanta Yana Yi Wa Isra’ila Aiki

Babban magatakardar kungiyar Hizbullah Sheikh Na’im Kassim ya bayyana cewa; Hizbullah tana yin aiki ne ta fuskoki biyu; na farko gwgawarmaya da HKI, sai kuma a fagen Siyasa a cikin gida.

Shugaban kungiyar ta Hizbullah wanda ya gabatar da jawbai a jiya domin girmama babban kwamandan kungiyar Hizbullah Shahid Sayyid Fu’ad Shukr ya ce; An zabi shugaban kasa Joseph Aun ne bayan da aka dauki shekaru ba tare da shugaban kasa ba a kasar. Kuma kungiyar gwagwarmaya ta tabbatar da cewa ginshiki ne a fagen siyasa, wacce ta saukaka yadda aka zabi shugaban kasar da kafa gwamnati.”

Har ila yau Sheikh Naim Kassim ya yi bayani akan yadda gwagwarmaya ta kafu a cikin kasar Lebanon a matsayin mayar da martani ga mamayar HKI, ta kuma cike gibin da sojoji su ka bari, da a karshe a 2000 ta kori HKI daga cikin Lebanon.

Sheik Na’im Kassim ya kuma ce; Gwgawarmaya wani nauyi ne da rataya akan kowa, ba wai zabi ba ne,kuma lokacin da aka yi aiki a tsakanin gwgawarmaya, soja da al’umma an cimma nasarori masu yawan gaske.

Babban  magatakardar kungiyar ta Hizbullah sheik Na’im Kassim ya kuma ce; Batun makaman dake hannun kungiyar Hizbullah wani batu ne da ya shafi cikin gidan kasar Lebanon, don haka ba shi da wata alaka da HKI.”

Akan batun kwance damarar yakin kungiyar ta Hizbullah, Sheikh Na’im Kassim ya ce, duk wanda yake son ganin hakan ta faru, to yana yi wa Isra’ila aiki ne.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Mata July 31, 2025 Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila July 31, 2025 Kasar Iran Ta Bayyana Gushewar Hasashen Raunin Karfin Sojinta Kuma Ba Zai Dawo Ba July 31, 2025 Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine July 31, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku   July 31, 2025 Qolibaf: Barin HKI Ta Yi Abinda Taga Dama Ne Yana Karfafa Mata Giwa July 30, 2025 Yunwa Ta Kashe Karin Falasdinawa 7 A Gaza July 30, 2025 Malta Zata Amince da Samuwar Falasdinu a Cikin Watan Satumba Mai Zuwa July 30, 2025 Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah July 30, 2025 Siriya Da HKI Zasu Gudanar Da Taro A Baku July 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Ta Kakabawa Jami’an Gwamnatin Falasdinawa Takunkuman Hana Shiga Amurka
  • Ministan Harkokin Wajen Siriya Yana Rasha Don Bude Sabon Shafi Tsakaninsu
  • Kassim: Duk Wanda Yake Neman Hizbullah Ta Ajiye Makamanta Yana Yi Wa Isra’ila Aiki
  • Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku  
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Amincewa Da Kasar Falasɗinu: Birtaniya Ta Gindaya Wa Isra’ila Sharuɗɗa
  • Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACF
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
  •  Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta
  • Rasha Ta Mayar Da Martani Ga Shugaban Amurka Kan Gindaya Wa’adin Kawo Karshen Yakin Ukraine