Shugaban Amurka Ya Ce: Sun Baiwa Fira Ministan Gwamnatin Isra’ila Damar Ya Aikata Abin Da Yake So
Published: 18th, February 2025 GMT
Shugaban kasar Amurka ya bayyana cewa: Fira ministan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ya aikata duk abin yake so
Shugaban Amurka Donald Trump ya yi nuni da wa’adin da ya bayar dangane da yarjejeniyar tsagaita bude wuta da kuma sakin fursunonin, yana mai cewa ya shaidawa fira ministan gwamnatin mamayar Isra’ila Benjamin Netanyahu ya aika duk abin da yake so.
Trump ya tabo batun mataki na gaba – ana sa ran za a fara tattaunawa nan ba da jimawa kan kashi na biyu na yarjejeniyar – ya ce: “Ya rage ga gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila kan mataki na gaba, tare da tuntubarsa.”
An kuma tambayi Trump ko jinkirin jigilar makamai zuwa haramtacciyar kasar Isra’ila a karkashin Shugaba Biden zai “hana tsagaita bude wuta?,” inda ya amsa da cewa: “Wannan ana kiransa zaman lafiya ta hanyar karfi.
Kalaman na zuwa ne bayan da Netanyahu ya sanar da cewa zai kira taro domin tattaunawa kan mataki na biyu na yarjejeniyar da ya kamata a bude makonni biyu da suka gabata.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza
Kwamitin bincike mai zaman kansa na Majalisar Dinkin Duniya, ya fitar da wani rahoto mai zargin Isra’ila da laifin aikata kisan kiyashi a zirin Gaza.
A cikin sabon rahoto da ta gabatar a ranar Talata, MDD ta zargi shugaban kasar Isra’ila Isaac Herzog, da firaministan kasar Benjamin Netanyahu, da kuma tsohon ministan tsaro Yoav Gallant da “kimsa kisan kiyashi.”.
Rahoton ya tattara batutuwan da suka shafi farar hula kai tsaye, ciki har da yara, ya kuma bayyana cewa kisan kiyashin da ake yi ya fi yawa fiye da yadda aka yi tashe-tashen hankula a baya.
Masu binciken sun kuma tabbatar da cewa da gangan Isra’ila ta haifar da yanayin da ke barazana ga rayuwar Falasdinawa ta hanyar toshe hanyoyin samun muhimman kayayyaki na wannan al’umma.
Rahoton ya biyo bayan wani bincike da aka yi na tsawon shekaru biyu, kuma ya yi nuni da yadda ayyukan Isra’ila ke a matsayin kisan kare dangi.
A martanin da ta mayar, Isra’ila ta yi watsi da sakamakon binciken da cewa “karya ce “, ta kuma bukaci da a rusa hukumar nan take.
A sa’i daya kuma, kwamitin bincike na MDD ya yi kira ga kasashe da su daina baiwa Isra’ila makamai da kayan aikin da za a iya amfani da su wajen aikata kisan kare dangi.
Fitar da rahoton na zuwa ne mako guda gabanin babban taron Majalisar Dinkin Duniya a birnin New York, inda ake sa ran kasashe da dama za su amince da kasar Falasdinu a hukumance.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran da Saudiyya sun bukaci hadin Musulmi game da halin da ake ci a yankin September 17, 2025 Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza September 17, 2025 Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza September 17, 2025 Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza. September 16, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaida Dake Yamen September 16, 2025 Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki 5 A Wajen Taron kere-kere . September 16, 2025 Iran Ta Bukaci IAEA Tayi Tir Da Harin Da Isra’ila Ta Kai A Tashoshin Nukiyarta. September 16, 2025 Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana September 16, 2025 Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi September 16, 2025 Pezeshkian: Ta’addancin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Kan Kasar Qatar Zalunci Ne Ga Diflomasiyya September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci