Janye Tallafin Amurka Ya Jefa Masu Fama Da Cutar HIV A Kasar Afirka Ta Kudu Cikin Fargaba
Published: 18th, February 2025 GMT
Wasu daga cikin mutanen kasar Afirka ta kudu da suke dauke da cutar HIV suna yin koken cewa janye tallafin da Amurka ta yi a karkashin hukumar nan ta USAID, zai jefa rayuwarsu a tsakanin mutuwa da rayuwa.
Da akwai miliyoyin mutane a kasar ta Afirka Ta Kudu da suke dauke da cutar HIV da su ka cutu daga dakatar da ayyukan hukumar USAID akan kiwon lafiya.
Yankin KwaZulu-Natal dake kasar Afirka ta kudu, yana da masu fama da cutar ta HIV da sun kai miliyan 1.9 a bisa kididdigar 2022. A fadin kasar kuwa da akwai masu dauke da wannan cutar da sun haura miliyan 7.5 da shi ne adadi mafi girma a duniya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
A nata bangare kuwa, Amurka ta bayyana aniyarta ta aiki tare da bangaren Sin, wajen ci gaba da warware sabani a fannonin tattalin arziki da cinikayya ta hanyar tsarin gudanar da shawarwari, da ingiza damar samar da karin nasarori daga tattaunawar, da kara samar da daidaito a alakar tattalin arziki da cinikayya tsakaninta da Sin.
Wakilin cinikayya na kasa da kasa na Sin karkashin ma’aikatar cinikayya, kuma mataimakin ministan cinikayyar kasar Li Chenggang, ya bayyana a yayin da yake yiwa manema labarai karin haske game da zaman tattaunawar sassan biyu. Ya ce sassan biyu suna sane da muhimmancin wanzar da daidaito, da kyautata alakar tattalin arziki mai nagarta tsakanin Sin da Amurka, sun kuma yi kyakkyawar musaya game da muhimman batutuwan cinikayya da na raya tattalin arziki dake jan hakulansu. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp