Za A Iya Samun Biliyoyin Daloli A Noman Zogale Da Kantu A Tekun Chadi
Published: 16th, February 2025 GMT
A cewarsa, sama da mutane miliyan uku rikice-rikicen ta’addanci ya tilasta su yin kaura da daga matsugunansu.
Har ila yau, ya shawarci kungiyoyin da ke yankin; kan bukatar yin hadin kai mai karfi da samar da tsare-tsaren da za su habaka aikin noma da kiwon Kifi a yankin.
.এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya amince da naɗa Muhammad Fa’iz a matsayin Kwamanda Janar na farko na Hukumar Hisbah ta Jihar.
Sakataren Gwamnatin Jihar Jigawa, Malam Bala Ibrahim, ne ya tabbatar da naɗin ga manema labarai a Dutse.
Ya bayyana cewa hakan na daga cikin ƙoƙarin Gwamna Namadi na ƙarfafa ayyukan sabuwar hukumar Hisbah da inganta aikinta.
A cewar sa, naɗin ya haɗa da Dr. Husaini Yusuf Baban a matsayin Babban Mataimakin Kwamanda Janar, da Lawan Danbala a matsayin Mataimakin Kwamanda Janar da hedikwatar hukumar, da kuma Yunusa Idris Barau a matsayin Mataimakin Kwamanda Janar naYankin Dutse.
Sauran su ne Abdulkadir Zakar, Mataimakin Kwamanda Janar, Yankin Hadejia, da Suraja Adamu, Mataimakin Kwamanda Janar, Yankin Gumel, da Bello Musa Gada, Mataimakin Kwamanda Janar, Yankin Kazaure, sai Barrister Mustapha Habu a matsayin Sakatari kuma Lauya mai ba da shawara.
Malam Bala Ibrahim ya jaddada cewa an zaɓi waɗannan mutane ne bisa cancanta, ƙwarewa da kuma nagartar halayensu, yana mai kira gare su da su yi kokarin sauke nauyin da aka dora musu.
Sakataren Gwamnatin Jihar ya ce an riga an mika musu takardun naɗi kuma sun shirya tsaf don fara aiki nan take.
A nasa bangaren, Muhammad Fa’iz ya gode wa Gwamna bisa amincewar da ya nuna musu, tare da alƙawarin gudanar da aiki da ƙwazo da himma.
Usman Muhammad Zaria