Leadership News Hausa:
2025-08-02@02:15:04 GMT

Wasu ‘Yan Bindiga Sun Bindige Fasto A Gombe

Published: 15th, February 2025 GMT

Wasu ‘Yan Bindiga Sun Bindige Fasto A Gombe

A nasa jawabin, Jatau ya bayyana cewa, duk da cewa kisan da aka yi wa wani malamin addini lamari ne mai ban tausayi, amma babu wata kwakkwarar shaida da ke alakanta lamarin da wata kungiya, addini ko kabilanci.

Ya tuna irin abubuwan da suka faru a baya inda daga baya aka gano wadanda suka aikata laifin ‘yan kungiya daya ne ko kabila ko addini.

Jatau ya kuma umarci jami’an tsaro da su kama wadanda ke da hannu a kisan tare da tabbatar da an hukunta su. Ya bukaci shugabanni da su kasance masu kamun kai da hakuri wajen tafiyar da irin wadannan al’amura masu muhimmanci domin hana faruwar lamarin.

“Ina kira gare ku a matsayinku na shugabanni da ku yi hakuri, ku kwantar da hankalin ku, ku yi tsayin daka har sai an kama masu laifin. Za ku iya tunawa a wani lokaci da ya wuce lokacin da aka kashe wani Fasto kuma daga baya aka gano cewa masu laifin ’yan coci daya ne. Kwanan nan an samu kashe-kashe a garin Kuri da ke karamar Hukumar Yamaltu-Deba kuma abin da ake magana a kai shi ne Fulani makiyaya ne amma daga baya aka gano cewa ba Fulani ne masu laifin ta kowace hanya ba,” in ji shi.

Shugaban kungiyar Kiristoci ta Nijeriya, Rabaran Joseph Alphonsus Shinga, tare da shugaban ECWA reshen arewa maso gabas, Reberend Isa Uba, da shugaban DCC na Gombe, Reb Dr Adamu Dauda, sun kuma jajantawa al’ummar Kirista da su kalli lamarin a matsayin wani bangare na kalubalen da masu bi ke fuskanta. Sun jadadda cewa irin wadannan bala’o’i suna tunatar da bukatar dogara ga shirin Allah.

Shugaban kungiyar ta CAN ya tabbatar wa al’umma cewa gwamnatin jihar ta nuna bakin cikin su kuma ta himmatu wajen ganin an kamo masu laifin. Shugaban hukumar ta DCC ya nuna jin dadinsa ga yadda gwamnati da jami’an tsaro suka dauki matakin gaggawa bayan faruwar wannan mummunan lamari.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ƴan Bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda ’yan bindiga suka tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina

’Yan bindiga sun tarwatsa kauyuka sama da 10 da ke zagaye da ƙaramar hukumar Bakori ta jihar Katsina sannan suka mayar da sama da 6,000 ’yan gudun hijira.

Maharan dai sun rika kashe mazauna kauyukan sannan su sace wasu su yi garkuwa da su domin karɓan kuɗin fansa.

Bayanai na cewa a ’yan kwanakin nan, ’yan bindigar na cin karensu babu babbaka a inda suka tarwatsa kauyuka kamar su Guga da Kandarawa da Kakumi da kuma Monono.

Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACF DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure

Har ila yau lamarin ya shafi ƙauyukan anguwar ’Yar Dabaru da anguwar Ɗan Marka, da Sabon Gida da ƙauyan Doma da dai sauran su.

Hakan dai ya haifar da kauracewa ƙauyukan ga mazaunansu da suke da sauran numfashi inda a yanzu haka ake da ’yan gudun hijira sama da 3,500 da ke neman mafaka a cikin garin Bakori.

Kazalika, rahotanni sun kuma ce akwai wasu sama da 2,500 da ke garin Guga don neman mafaka.

’Yan gudun hijirar wadanda akasarinsu mata ne da ƙananan yara sun watsu a wurare daban daban.

Aminiya ta zagaya unguwan Kafaɗi da unguwar Ma’aru da ke Sabuwar Abuja a cikin garin na Bakori, inda wakilinmu ya tarar da cincirindon mata da ƙananan yara a rakuɓe, a gidajen ’yan uwa, wasu kuma a makarantun firamaren gwamnati da ke karamar hukumar ta Bakori.

A tattaunawar Wakilinmu da wasu daga cikin ’yan gudun hijira wadanda suka fito daga kauyaku daban-daban na jihar, sun nuna alhininsu game da yadda ’yan bindigar ke cin karensu ba babbaka a yankin.

Imrana Shafi’u wanda ’yan bindigar suka harbe shi a ƙafa har wuri biyu, wanda shi ya yi hijira ne daga kauyan Ɗan Marka, ya ce lamarin na da ban tsoro matuƙa.

A cewarsa, “Ni ma Allah ne ya sa zan rayu domin ’yan bindigan sun zaci na mutu ne.

“Domin da suka zo kanmu harbin kan mai uwa da wabi, suka yi ta yi, inda suka kashe mutane da dama.

“Ni ma dai Allah ne ya tsirar dani, domin duk wadanda nake tare da su duk an kashe su, ni kadai na tsira cikin ikon Allah,” in ji shi.

Ita kuwa Malama Marawiya wacce ta yi gudun hijira daga kauyan ’Yar Dabaru ta ce da rana tsaka ’yan bindiga suka keto cikin kauyan nasu, suka tarwatsasu sa’ilin da suka tasa ƙeyar mata sama da 10 kuma duk yawancinsu suna ɗauke da goyo suka yi cikin daji da su.

Marawiya ta kara da cewa kusan kwanakin matan 10 ke nan a hannun su kuma sun ce sai an biya kudin fansa har Naira miliyan daya da rabi kan kowanne mutum daya kafin a sake su.

Ta Kara da cewa “A da in suka dauki mutum bai wuce su ce a ba su Naira dubu ɗari biyar ba amma a wannan karon sai suka ce sai an biya har sama da naira miliyan daya da rabi ga kowanne mutum,” in ji ta.

Yusuf Usman, wanda suka yi sansani a wata makarantar Firamare ta Nadabo da ke cikin garin Bakori, ya ce kusan su ɗari uku ne suka yi gudun hijira daga kauyan Doma, cikinsu har da tsofaffi.

Ya kuma ce, “A haka muka tako da ƙafa muka yini muna tafiya tare da mata da yaran kanana har Allah ya kawo mu garin Bakori,” in ji shi.

Ya kara da cewa kusan shekara biyar kenan suna fama da wannan matsalar ta tsaro, kuma ba dare ba rana bare damina ko rani, haka ake shigowa kauyakun su ana kashe su sannan kuma a tasa ƙeyar su a tafi da su daji domin karɓan kuɗin fansa.

Shugaban kwamitin da ƙaramar hukumar Bakori ta kafa domin kula da ’yan gudun hijirar, Mallam Mamman Yaro Bakori, ya ce adadin ’yan gudun hijirar sun kai 3,500 a garin Bakori.

Ya Kara da cewa a garin Guga Kuma akwai akalla kimanin mutane 2,500 da suke gudun hijira a can.

Shugaban ya ce kuma kusan a kullum yawan su ƙaruwa yake yi, sannan suna warwatse ne a wurare daban daban a inda wasu suke zaune a gidajen ‘yan uwansu wasu kuma suna zaune ne a makarantar firamare ta Nadabo a cikin garin Bakori.

Sai dai ya ce tuni Shugaban ƙaramar hukumar Bakori, Abubakar Barde ya bayar da umurnin kai masu tallafin kayan abinci sau uku a rana tare da kudin cefane don saukaka masu rayuwar da suke ciki.

Wasu na bayyana cewa a ‘yan kwanakinnan ’yan bindigar na cin karensu babu babbaka a inda suka kafa sansaninsu a dajin Guga da Kandarawa da Kakumi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
  • NBRDA Za Ta Hada Gwiwa Da KIRCT Domin Habaka Magunguna Da Yaki Da Cututtuka
  • Gaza: Mutane Da Dama Sun Yi Shahada A Yau Wasu Kuma Sun Jikkata
  • Hare-hare: ’Yan bindiga sun raba mutum 5,000 da muhallansu a Katsina
  • Wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu saboda ɗan Kudu ne — Onanuga
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Yadda ’yan bindiga suka tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja
  • Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga