Leadership News Hausa:
2025-09-17@23:26:25 GMT

Wasu ‘Yan Bindiga Sun Bindige Fasto A Gombe

Published: 15th, February 2025 GMT

Wasu ‘Yan Bindiga Sun Bindige Fasto A Gombe

A nasa jawabin, Jatau ya bayyana cewa, duk da cewa kisan da aka yi wa wani malamin addini lamari ne mai ban tausayi, amma babu wata kwakkwarar shaida da ke alakanta lamarin da wata kungiya, addini ko kabilanci.

Ya tuna irin abubuwan da suka faru a baya inda daga baya aka gano wadanda suka aikata laifin ‘yan kungiya daya ne ko kabila ko addini.

Jatau ya kuma umarci jami’an tsaro da su kama wadanda ke da hannu a kisan tare da tabbatar da an hukunta su. Ya bukaci shugabanni da su kasance masu kamun kai da hakuri wajen tafiyar da irin wadannan al’amura masu muhimmanci domin hana faruwar lamarin.

“Ina kira gare ku a matsayinku na shugabanni da ku yi hakuri, ku kwantar da hankalin ku, ku yi tsayin daka har sai an kama masu laifin. Za ku iya tunawa a wani lokaci da ya wuce lokacin da aka kashe wani Fasto kuma daga baya aka gano cewa masu laifin ’yan coci daya ne. Kwanan nan an samu kashe-kashe a garin Kuri da ke karamar Hukumar Yamaltu-Deba kuma abin da ake magana a kai shi ne Fulani makiyaya ne amma daga baya aka gano cewa ba Fulani ne masu laifin ta kowace hanya ba,” in ji shi.

Shugaban kungiyar Kiristoci ta Nijeriya, Rabaran Joseph Alphonsus Shinga, tare da shugaban ECWA reshen arewa maso gabas, Reberend Isa Uba, da shugaban DCC na Gombe, Reb Dr Adamu Dauda, sun kuma jajantawa al’ummar Kirista da su kalli lamarin a matsayin wani bangare na kalubalen da masu bi ke fuskanta. Sun jadadda cewa irin wadannan bala’o’i suna tunatar da bukatar dogara ga shirin Allah.

Shugaban kungiyar ta CAN ya tabbatar wa al’umma cewa gwamnatin jihar ta nuna bakin cikin su kuma ta himmatu wajen ganin an kamo masu laifin. Shugaban hukumar ta DCC ya nuna jin dadinsa ga yadda gwamnati da jami’an tsaro suka dauki matakin gaggawa bayan faruwar wannan mummunan lamari.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ƴan Bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare

Fitattun dalibai akalla 12 ne  daga makarantun gwamnati suka samu guraben tallafin karatun sakandare  a ƙarƙashin Asusun Tallafin Karatu na Jihar Kwara (Kwara-ETF).

A wajen taron gabatarwa ga waɗanda suka fara cin moriyar shirin, Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq ya bayyana cewa ci gaban harkar ilimi a Najeriya abu ne mai tsada kuma ya zama wajibi kowa ya bayar da gudummawarsa.

Ya roƙi masu masu hannu da shuni da kungiyoyi masu zaman kansu da su tallafa wajen gina makarantu ko kuma su ɗauki nauyin daliban da suka nuna bajinta da jajircewa a harkar karatu.

A cewarsa, an zabo daliban 12 ne  sakamakon bajintar da suka nuna a matakai daban-daban na tantancewa da Kwara ETF ta gudanar.

Gwamnan ya bayyana cewa tallafin ya kunshi dukkan kuɗin da ake buƙata a karatun sakandaren daliban.

“Muna kira da jama’a su ba da gudummawa da kuma ɗaukar nauyin ɗalibai. Kada a bar wannan aiki ga gwamnati da iyaye kadai. Ilimantar da ‘ya’yanmu hakki ne da ya rataya a kanmu gaba ɗaya,” in ji Gwamna.

Ya yaba da tsarin zaɓen kuma ya taya waɗanda suka yi nasara murna.

A nata jawabin, Babbar Shugabar Kwara ETF, Oluwadamilola Amolegbe, ta ce daliban 12 sun fito ne daga cikin jerin ɗalibai 640 da aka fara tantancewa bisa cancanta.

Ta bayyana cewa tsarin zaɓen ya fara ne da rubuta jarabawa ga dukkan daliban firamare na aji shida da suka amfana da shirin KwaraLEARN na koyon fasahar zamani, har zuwa lokacin da aka kammala tantancewa.

 

Ali Muhammad Rabi’u 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa