Dalilin da ’yan siyasa ke sauya sheƙa zuwa APC — Tambuwal
Published: 15th, February 2025 GMT
Tsohon Gwamnan Sakkwato, Aminu Waziri Tambuwal, ya bayyana cewa guguwar sauyin sheƙa da ta fara kaɗawa a tsakanin jam’iyyun siyasa a Arewa maso Yammacin ƙasar na da alaƙa na son zuciyar ’yan siyasar yankin.
Tambuwal ya bayyana hakan ne yayin ganawa da manema labarai a taron ƙusoshin jam’iyyar PDP da ya gudana yau Asabar a Jihar Kaduna.
Tambuwal ya zargi ’yan siyasar da ke sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC mai mulki a ƙasar da son zuciya waɗanda ya ce ba sa kishin al’umma.
Tsohon gwamnan ya ce akwai dalilai da ’yan siyasa ke sauya sheƙa daga wannan jam’iyyar zuwa wata, “sai dai abin da na fahimta shi ne galibi ’yan siyasar na yin hakan ne ba don kishin al’umma ba face sai don buƙatunsu na ƙashin kai.
“Sannan kuma a yanzu duk wani ɗan siyasar da ya san abin da ya kamata, ba zai koma jam’iyyar APC ba saboda ƙuncin rayuwa da Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta jefa ’yan Nijeriya a ciki.
Tambuwal wanda ƙusa ne a jam’iyyar PDP a Nijeriya, ya caccaki Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin APC da cewa ba ta wata madafar kamawa ballanta sanin inda ta dosa haɗi da rashin tausayin ’yan ƙasar.
Sanatan Sakkwato ta Kudu ya yi kira ga duk jam’iyyun adawa a ƙasar da su haɗa ƙarfi domin kawo wa ’yan Nijeriya sauyin da suke buƙata a Zaɓen 2027.
Aminiya ta ruwaito cewa, daga cikin manyan ’yan siyasar da suka halarci taron akwai tsohon Gwamnan Kaduna, Sanata Ahmed Makarfi da takwaransa na Kano, Sanata Ibrahim Shekarau da tsohon ɗan takarar Gwamnan Jigawa, Mustapha Sule Lamido da Sanata Lado Dan Marke, da Honarabul Isa Ashiri Kudan da Ango Abdullahi da Shugaban Matasa na PDP, Muhammad Kadade Suleiman da sauransu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Aminu Waziri Tambuwal zaɓen 2023 Zaɓen 2027 yan siyasar
এছাড়াও পড়ুন:
Mutanen da talauci ya yi wa katutu zai ƙaru a Nijeriya — Bankin Duniya
Bankin Duniya ya yi hasashen cewa adadin waɗanda talauci ya yi wa katutu a Nijeriya zai ƙaru zuwa kaso 3.6 cikin ɗari a 2027.
Wannan dai na ƙunshe ne cikin wani rahoto da Bankin Duniya ya fitar game da tattalin arziki da kuma yanayin tsadar rayuwa a Nijeriya.
Ɗaukewar wutar lantarki ta tsayar da al’amura a Sifaniya da Portugal Talata ce ɗaya ga watan Zhul Qi’ida — Sarkin MusulmiBankin Duniya ya fitar da rahoton ne bayan ganawa tsakanin wakilansa da na Asusun Bada Lamuni na Duniya IMF kamar yadda RFI ya ruwaito.
Rahoton ya ce dogaro da Nijeriya ta yi gaba ɗaya kan man fetur na ɗaya daga cikin dalilin da zai sa haɓakar tattalin arzikinta ya ci gaba da tafiyar hawainiya.
Bankin Duniyar ya ce har yanzu mahukuntan Nijeriya ba su ɗauko hanyar fitar da ingantattun tsare-tsaren tattalin arziki da za su taimaki talakawan ƙasar ba.
A cewarsa, abin takaici ne yadda talakawan ƙasashe masu tarin albarkatu ke fama da talauci saboda rashin mayar da hankali daga shugabanni.
Bankin ya ce duk da ci gaban da Nijeriya ta samu a sauran fannonin da ba na man fetur ba musamman a bara, amma duk da haka babu alamar samun ci gaba a ɓangaren tattalin arzikin talakawan ƙasar ta yammacin Afirka.
Rahoton ya jaddada cewa har yanzu yankin ƙasashen Sahel ne ke kan gaba a talauci a duniya gaba ɗaya, yayin da yankin ke da kaso 80 adadin mutane miliyan 695 na mutanen da ke fama da baƙin talauci.