Aminiya:
2025-06-16@00:56:48 GMT

Dalilin da ’yan siyasa ke sauya sheƙa zuwa APC — Tambuwal

Published: 15th, February 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Sakkwato, Aminu Waziri Tambuwal, ya bayyana cewa guguwar sauyin sheƙa da ta fara kaɗawa a tsakanin jam’iyyun siyasa a Arewa maso Yammacin ƙasar na da alaƙa na son zuciyar ’yan siyasar yankin.

Tambuwal ya bayyana hakan ne yayin ganawa da manema labarai a taron ƙusoshin jam’iyyar PDP da ya gudana yau Asabar a Jihar Kaduna.

Ɗan Nijeriya ya lashe kyautar Kundin Bajinta na Duniya a fagen ɗaukar hoto Makwabta sun kai karar ma’aurata saboda carar zakaransu

Tambuwal ya zargi ’yan siyasar da ke sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC mai mulki a ƙasar da son zuciya waɗanda ya ce ba sa kishin al’umma.

Tsohon gwamnan ya ce akwai dalilai da ’yan siyasa ke sauya sheƙa daga wannan jam’iyyar zuwa wata, “sai dai abin da na fahimta shi ne galibi ’yan siyasar na yin hakan ne ba don kishin al’umma ba face sai don buƙatunsu na ƙashin kai.

“Sannan kuma a yanzu duk wani ɗan siyasar da ya san abin da ya kamata, ba zai koma jam’iyyar APC ba saboda ƙuncin rayuwa da Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta jefa ’yan Nijeriya a ciki.

Tambuwal wanda ƙusa ne a jam’iyyar PDP a Nijeriya, ya caccaki Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin APC da cewa ba ta wata madafar kamawa ballanta sanin inda ta dosa haɗi da rashin tausayin ’yan ƙasar.

Sanatan Sakkwato ta Kudu ya yi kira ga duk jam’iyyun adawa a ƙasar da su haɗa ƙarfi domin kawo wa ’yan Nijeriya sauyin da suke buƙata a Zaɓen 2027.

Aminiya ta ruwaito cewa, daga cikin manyan ’yan siyasar da suka halarci taron akwai tsohon Gwamnan Kaduna, Sanata Ahmed Makarfi da takwaransa na Kano, Sanata Ibrahim Shekarau da tsohon ɗan takarar Gwamnan Jigawa, Mustapha Sule Lamido da Sanata Lado Dan Marke, da Honarabul Isa Ashiri Kudan da Ango Abdullahi da Shugaban Matasa na PDP, Muhammad Kadade Suleiman da sauransu.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Aminu Waziri Tambuwal zaɓen 2023 Zaɓen 2027 yan siyasar

এছাড়াও পড়ুন:

Abokin Takarar Tinubu: Rikici ya ɓarke a APC bayan Ganduje ya ƙi goyon bayan Shettima

An samu saɓani a wani taron shugabannin jam’iyyar APC a yankin Arewa Maso Gabas da aka gudanar a Jihar Gombe.

Rikicin ya fara ne bayan da Kwamared Mustapha Salihu, Mataimakin Shugaban APC na ƙasa mai kula da Arewa Maso Gabas, ya bayyana goyon bayansa ga takarar Shugaba Bola Tinubu don ya sake tsayawa takara a karo na biyu.

Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensa HOTUNA: Yadda aka yi sulhu da ƙasurgumin ɗan fashin daji Ado Aliero a Katsina

Sai dai bai ambaci mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima ba.

Manyan jiga-jigan jam’iyyar APC daga yankin sun halarci taron, ciki har da gwamnoni, ministoci, da ‘yan majalisa.

Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Ganduje, shi ma ya halarci taron.

Bayan Salihu ya gama jawabi, wasu daga cikin mahalarta taron sun fusata.

Take suka fara yi masa ihu, wasu ma suna barazanar kai masa hari.

Sai jami’an tsaro sun fito da shi daga ɗakin taron don kare lafiyarsa.

Don kwantar da rikicin da ya taso, Mataimakin Shugaban jam’iyyar na ƙasa, Bukar Dalori, ya fito ya bayyana goyon baya ga Tinubu da kuma Shettima don su ci gaba da mulki.

Amma lamarin ya ƙara dagulewa bayan da Ganduje ya yi jawabi, inda ya ayyana goyon bayansa ga Tinubu kaɗai, ba tare da ya ambaci Shettima ba.

A yayin jawabin da ya yi na kusan minti 10, bai ambaci sunan Shettima ba.

Shi ma sai da jami’an tsaro suka fita da shi daga wajen taron saboda gudun rikicin da zai je ya dawo.

Shettima dai ɗan Jihar Borno ne, ɗaya daga cikin jihohin yankin Arewa Maso Gabas.

Mutane da dama sun ji ba ɗadi kan rashin ambaton sunan a wajen taro da aka yi a yankinsa.

Taron ya kare cikin gaggawa saboda tashin hankali.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Kasar Iran Sun Ce Bazasu Dakatar Da Yaki ba Har Zuwa Samun Nasara A kan HKI
  • Cece-Kuce Ya Barke Bayan Ganduje Da Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas Sun Nemi A Sauya Shettima A 2027
  • Takarar Tinubu: Rikici ya ɓarke a APC bayan Ganduje ya ƙi goyon bayan Shettima
  • Abokin Takarar Tinubu: Rikici ya ɓarke a APC bayan Ganduje ya ƙi goyon bayan Shettima
  • Dalilin da muka soke tattaunawar nukiliya da Amurka — Iran
  • HKI Ta Rufe Filin Saukar Jiragen Sama Na Ben Gorion Tare Da Dauke Jiragenta  Zuwa Waje
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya
  • An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia
  • Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje