Aminiya:
2025-09-18@02:17:14 GMT

Bidiyon TikTok: Jami’ar UNIZIK ta kori ɗalibar da ta ci kwalar malami

Published: 14th, February 2025 GMT

Hukumomin Jami’ar Nnamdi Azikiwe (Unizik) da ke, Awka a Jihar Anambra ta kori ɗalibar nan mai suna Goddy-Mbakwe Chimamaka Precious, saboda cin kwalar wani malamin jami’ar Dakta Chukwudi Okoye.

A cikin wani bidiyo da ya karaɗe shafukan sada zumunta an ga Goddy-Mbakwe ta far wa malamin jami’ar, Dakta Chukwudi bayan ya ratsa ta cikin bidiyon da take ɗauka a wani wuri da ke harabar jami’ar.

An ɗage taron mahaddata Qur’ani da za a yi a Abuja Asabar za a yi zaɓen ƙananan hukumomin Katsina

A cikin takardar korar ɗalibar da jami’ar ta fitar mai ɗauke da kwanan watan 13 ga watan Fabrairu, wanda muƙaddashin magatakardar jami’ar, Ɓictor I. Modebelu ya sanya wa hannu, ta ce an ɗauki matakin korar ne bayan shawarar kwamitin bincike da jami’ar ta yi.

Hukumar jami’ar ta ce ”Kwamitin ya samu ɗalibar da laifin saɓa wa dokokin ladabtarwa na jami’ar, musamman sashe na 4 na dokar ladabtarwa ta (SDR)”, in ji takardar korar.

Bidiyon cin kwalar malamin ya ja hankalin mutane da dama a shafukan sada zumunta, inda aka yi ta kiraye-kirayen ɗaukar mataki kan lamarin.

Hukumar Jami’ar ta buƙaci ɗalibar da ta gaggauta ficewa daga harabar jami’ar tare da mayar wa jami’ar duk wasu abubuwan da ke hannun ɗalibar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: ɗalibar da

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi

Wasu mutum shida sun shiga hannun ’yan sanda kan zargin satar zinari da kuɗinta ya haura Naira miliyan 109.5 a Jihar Kebbi.

Sashen binciken manyan laifuka na rundunar ’yan sanda a jihar Kebbi na tuhumar su da sace sarkoƙin zinare guda biyar sauran kayan zinare daga wani gida a garin Ka’oje, Ƙaramar Hukumar Bagudo.

Sauran sun haɗa da zobba huɗu da munduwar hannu tara, da nauyinsu ya kai gram 782.7 — dukkansu mallakar ’ya’ya da ’yan uwar mai gidan.

Wanda ake tuhuma ya amsa laifi

Bayan samun koken, jami’an suka kama Ibrahim Abubakar Ka’oje, jami’i a Hukumar Gyaran Hali ta Kasa, wanda a yayin bincike, ya amsa laifin.

’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu

Ya bayyana cewa ya sayar da kayan ga wasu mutane biyu, dukkansu daga Sakkwato, tare da wasu mutum biyu a Jihar Kebbi.

An kuma gano wanda  ya taimaka masa wajen sayar da wasu daga cikin kayan, inda ya karɓi naira miliyan 2.5 a matsayin lada.

Rundunar ’yan sanda ta bayyana cewa har yanzu tana neman sauran da suka gudu, bisa zargin taimakawa wajen sayar da kayan sata.

Ana zargin an sayi filaye biyu a Birnin Kebbi da kuɗin da aka samu daga sayar da kayan.

Abubuwan da aka ƙwato

Kayan da aka ƙwato sun haɗa da munduwar hannu biyu, babur ɗin Haouje, da kuma wayoyin iPhone 16, Samsung Galaxy Ultra da Samsung Flip.

Kwamishinan ’yan sanda na Jihar Kebbi, Bello M. Sani, ya jinjina wa jajircewar jami’ansa bisa wannan nasara.

Ya kuma yi kira gare su da su ci gaba da aiki tukuru domin cafke sauran da ake nema da kuma ƙwato dukkan kayan da suka rage.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
  • Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin
  • Ɗangote zai gina ɗakunan kwanan ɗalibai 250  a Jami’ar Ilorin