Aminiya:
2025-05-01@04:16:14 GMT

Ta kacame tsakanin mahaifiyar 2Face da budurwarsa

Published: 14th, February 2025 GMT

Hakan dai ya faru ne dalilin baiko da fitaccen mawaƙin ya yi da ’yar majalisar jiha mai wakiltar Egor a jihar Edo, Natasha Osawuru, a wani bidiyo da ya karaɗe soshiyal midiya.

Ɓullar bidiyon ke da wuya mahaifiyar 2Face, Rose Idibia, ta fito a wani bidiyo tana roƙon duk wata uwa ta taya ta roƙon ‘yar majalisar ta karya asirin da ta yi wa ɗanta.

Kalaman mahaifiyar tasa dai na da nasaba da rabuwar 2Face da matarsa Annie da har yanzu bai kammala ba a hukumance.

Mahaifiyar tasa ta ce rashin haƙurin jiran aurensa ya rabu da tsohuwar matar tasa, da gaggawar neman auren ‘yar majalisar ne ya sanya ta gano cewa ɗan nata ba a hayyacinsa ya ke ba.

Tirela ta murƙushe mutane a Gadar Hotoro a Kano Masu noman tabar wiwi na barazanar ƙona gidajenmu —Makiyaya

Tun kafin auren 2Face da Annie wacce tsohuwar jarumar Nollywood ce sun sha yamutsa hazo, musamman haife-haife da 2Face ɗin ya yi da wasu matan biyu, duk da cewa suna tsaka da soyayya a lokacin.

Kazalika bayan auren rahoton soyayya da wasu matan bai tsaya ba, baya ga rigingimu tsakanin danginsa da Annie, da kuma zargin da ɗan uwanta ya yi mata na jefa shi a hanyar shaye-shaye.

Rahotanni dai na nuna sai da 2Face ya haifi ‘ya’ya huɗu da wasu matan kafin su yi aure, sannan suka haifi na biyar ɗin tare.
Idan za a iya tunawa dai, makonni da suka gabata ne 2Face ɗin ya fito ya ce zai rabu da tsohuwar matarsa Annie baya shekaru 12 da aure.

Sai dai daga baya ya fito ya ce masu kutse ne suka aikata hakan, bayan abokanan aikinsa da dama sun fito sun yi Alla-wadai da fito da zancen soshiyal midiya.

Kwanaki kaɗan bayan nan ne kuma ya sake yin bidiyo ya ce babu wani kutse da aka yi wa shafinsa, shi ne ya rubuta da kansa.
Jaridar Punch ta rawaito tsohuwar matar 2Face ɗin na wani wurin gyaran hali yanzu haka saboda fama da matsanancin shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da ta ke yi, kuma fitacciyar mawaƙiya Tiwa Savage na daga cikin masu kula da ita.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Natasha Osawuru Nollywood

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Da Iraki Sun Ce An Kammala Shimfida Layin Dogo Daga Shalamcheh Zuwa Basra

A wani taro wanda ya hada ministan riko na tattalin arziki da kudade na JMI da kuma mai bawa firai ministan kasar Iraki shawara, bangarorin biyu sun tabbatar da cewa an kammala aikin shimfida layin dogo tsakanin garin Shalamcheh na kasar Iran da kuma birnin Basra a kasar Iraki.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto jami’an gwamnatocin kasashen biyu na fadar haka, sun kuma jaddada muhimmancin layin dogon da kuma samar da kasuwar babu kudaden fito a kan iyakokin kasashen biyu.

Labarin ya kara da cewa harkokin kasuwanci tsakanin kasashen biyu ya zuwa yanzu ya kai dalar Amurka biliyon $11a ko wace shekara kuma anan saran nan gaba zai iyakaruwa zuwa dalar Amurka biliyon $25.

Rahmatollah Akrami, ministan riko na tattalin arziki da kudade na JMI, da kuma Hazem Majid Naji Al-Khalidi mai bawa firai ministan kasar Iraki shawara sun jaddada muhimmancin kammala layin dogo tsakanin kasashen biyu, da kuma kasuwar ba kudaden fito tsakanin kasashen biyu. Da kuma fatan zasu yi kokarin amfanar juna gwagwadon abinda zasu iya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Iran Da Iraki Sun Ce An Kammala Shimfida Layin Dogo Daga Shalamcheh Zuwa Basra
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa
  • Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai
  • Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci a Najeriya ya rasu
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi