Aminiya:
2025-07-31@19:07:47 GMT

Ta kacame tsakanin mahaifiyar 2Face da budurwarsa

Published: 14th, February 2025 GMT

Hakan dai ya faru ne dalilin baiko da fitaccen mawaƙin ya yi da ’yar majalisar jiha mai wakiltar Egor a jihar Edo, Natasha Osawuru, a wani bidiyo da ya karaɗe soshiyal midiya.

Ɓullar bidiyon ke da wuya mahaifiyar 2Face, Rose Idibia, ta fito a wani bidiyo tana roƙon duk wata uwa ta taya ta roƙon ‘yar majalisar ta karya asirin da ta yi wa ɗanta.

Kalaman mahaifiyar tasa dai na da nasaba da rabuwar 2Face da matarsa Annie da har yanzu bai kammala ba a hukumance.

Mahaifiyar tasa ta ce rashin haƙurin jiran aurensa ya rabu da tsohuwar matar tasa, da gaggawar neman auren ‘yar majalisar ne ya sanya ta gano cewa ɗan nata ba a hayyacinsa ya ke ba.

Tirela ta murƙushe mutane a Gadar Hotoro a Kano Masu noman tabar wiwi na barazanar ƙona gidajenmu —Makiyaya

Tun kafin auren 2Face da Annie wacce tsohuwar jarumar Nollywood ce sun sha yamutsa hazo, musamman haife-haife da 2Face ɗin ya yi da wasu matan biyu, duk da cewa suna tsaka da soyayya a lokacin.

Kazalika bayan auren rahoton soyayya da wasu matan bai tsaya ba, baya ga rigingimu tsakanin danginsa da Annie, da kuma zargin da ɗan uwanta ya yi mata na jefa shi a hanyar shaye-shaye.

Rahotanni dai na nuna sai da 2Face ya haifi ‘ya’ya huɗu da wasu matan kafin su yi aure, sannan suka haifi na biyar ɗin tare.
Idan za a iya tunawa dai, makonni da suka gabata ne 2Face ɗin ya fito ya ce zai rabu da tsohuwar matarsa Annie baya shekaru 12 da aure.

Sai dai daga baya ya fito ya ce masu kutse ne suka aikata hakan, bayan abokanan aikinsa da dama sun fito sun yi Alla-wadai da fito da zancen soshiyal midiya.

Kwanaki kaɗan bayan nan ne kuma ya sake yin bidiyo ya ce babu wani kutse da aka yi wa shafinsa, shi ne ya rubuta da kansa.
Jaridar Punch ta rawaito tsohuwar matar 2Face ɗin na wani wurin gyaran hali yanzu haka saboda fama da matsanancin shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da ta ke yi, kuma fitacciyar mawaƙiya Tiwa Savage na daga cikin masu kula da ita.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Natasha Osawuru Nollywood

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

Dangane da tattaunawar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka da aka gudanar a kwanan nan, Guo Jiakun ya bayyana cewa, ana fatan bangaren Amurka zai yi aiki tare da Sin wajen amfani da tsarin tattaunawa kan tattalin arziki da cinikayya tsakanin kasashen biyu, don sa kaimi ga bunkasa dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka cikin kwanciyar hankali.

Dangane da batun Falasdinu kuwa, Guo Jiakun ya ce, “manufar kafa kasashe biyu” ita ce hanya daya tilo ta hakika ta warware matsalar Falasdinu, kuma kasar Sin tana goyon bayan al’ummar Falasdinu wajen kafa kasa mai cin gashin kanta.(Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine
  • Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki
  • Rashin Nasarar DPP A Zagayen Farko Na Kuri’ar Kiranye Ya Nuna Rashin Amincewar Al’ummar Taiwan Da Salon Mulkin Jami’yyar
  • Shugabannin Hukumomin Watsa Labarai Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya ga Tsohuwar Uwargidan Shugaban Ƙasa Aisha Buhari
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata 
  • Araqchi: Iran Zata Mayar Da Martanin Da Ba Zai Yiwu A Boye Ba  Kan Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kanta
  • Kasar Iran Ta Musanta Yin Katsalandan A Tattaunawar Neman Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Rasha Ta Mayar Da Martani Ga Shugaban Amurka Kan Gindaya Wa’adin Kawo Karshen Yakin Ukraine
  • An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden