Noman rani ne zai kawar da yunwa a Yankin Tafkin Chadi — Zulum
Published: 12th, February 2025 GMT
Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum ya jaddada buƙatar samar da manyan gonakin gudanar da noman rani domin yaki da matsalar karancin abinci a Yankin Tafkin Chadi.
Gwamnan ya bayyana haka ne a yayin taron Gwamnonin Tafkin Chadi da aka gudanar makon da ya gabatar a garin Maiduguri fadar Jihar Borno karo na biyar, inda ya jadadda cewar, Allah SWT ya azurta wannan Yanki na Tafkin Chadi da dimbin filayen noma wanda idan aka yi amfani da su yadda ya kamata, na iya ba da gudummawa sosai wajen samar da abinci a yankin har ma da yankuna makwabta.
Zulum ya bayyana muhimmancin haɗin gwiwa tsakanin gwamnonin yankin da abokan haɗin gwiwa da Majalisar Dinkin Duniya domin kafa gonakin noman rani masu inganci.
Ya yi nuni da cewa dogaro da noman damina kadai ba zai dore ba, saboda karuwar al’ummar yankin, wanda ala tilas sai an hada da noman rani.
Zulum ya kuma jaddada bukatar yin bincike kan amfanin gona masu jure yanayi don tabbatar da isasshen abinci da wadatar abinci ga al’ummar wannan yanki.
Ya ba da shawarar cewa, shirin noman ranin zai iya tallafa wa ci gaban kiwon dabbobi, yadda za a samu wadataccen nama da kuma nono a yankin.
A cewar gwamnan, “kafa manyan gonakin noman rani na buƙatar jajircewa daga gwamnoni da abokan tarayya da gwamnatocin kasashenmu don ganin mun cim ma manufar hakan a kan lokaci, yadda al’ummomin za su amfana”, in ji shi.
Ya kuma jaddada cewa, “gabar Tafkin Chadi na samar da wadataccen ruwa, kuma ana iya haka rijiyoyi da sanya bututun tura ruwa inda ruwan ya yi ƙaranci don al’ummar wuraren su amfana.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Noman rani
এছাড়াও পড়ুন:
Girgizar Kasa Mai Karfi Ta Kada Yankin Kamtashatka Na Kasar Rasha
Rahotanni daga kasar Rasha sun ce girgizar kasa da ta kai karfin daraja 8.7 a ma’aunin Richard ta girgiza yankin Kamtashtka na kasar Rasha, da hakan ya sa kasashen yankin zama cikin zullumin afkuwar igiyar ruwan Tsunami.
Cibiyar da take kula da afkuwar girgizar kasa a turai ta ce, an yi girgizar kasar ne da misalin karfe 03;25 agogon Moscow, da hakan ya sa hukuma shelanta zama cikin halin ko-ta-kwana a yankin.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Yahudawa ‘Yan Share Wuri Zauna Sun Kutsa Cikin Masallacin Kudus July 30, 2025 Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka July 30, 2025 Shugaban Kasar Ivory Coast Ya Bayyana Shirinsa Na Sake Tsayawa Takarar Shugabanci Karo Na Hudu July 30, 2025 Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu July 30, 2025 MDD Zata Aiwatar Da Hanyar Warware Rikicin Falasdinawa Da Yahudawan Sahayoniyya July 30, 2025 Birtaniya Ta Yi Barazanar Amincewa Da Kasar Falasdinu A Watan Satumba Idan Yanayin Gaza Bai Canza Ba July 30, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Lod Da Ke Jaffa Da Makami Mai Linzami July 30, 2025 Faransa Ta Bayyana Wuce Gona Da Irin ‘Yan Sahayoniyya Kan Falasdinawa Da Ayyukan Ta’addanci July 30, 2025 Jagora: Iran Ta Bayyana Karfinta Da Jajircewarta A Yakin Kwanaki 12 Ga Duniya July 29, 2025 Mutum daya Yayi Shahada 4 Sun Ji Rauna Sanadiyar Hare-Haren HKI A Lebanon July 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci