Noman rani ne zai kawar da yunwa a Yankin Tafkin Chadi — Zulum
Published: 12th, February 2025 GMT
Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum ya jaddada buƙatar samar da manyan gonakin gudanar da noman rani domin yaki da matsalar karancin abinci a Yankin Tafkin Chadi.
Gwamnan ya bayyana haka ne a yayin taron Gwamnonin Tafkin Chadi da aka gudanar makon da ya gabatar a garin Maiduguri fadar Jihar Borno karo na biyar, inda ya jadadda cewar, Allah SWT ya azurta wannan Yanki na Tafkin Chadi da dimbin filayen noma wanda idan aka yi amfani da su yadda ya kamata, na iya ba da gudummawa sosai wajen samar da abinci a yankin har ma da yankuna makwabta.
Zulum ya bayyana muhimmancin haɗin gwiwa tsakanin gwamnonin yankin da abokan haɗin gwiwa da Majalisar Dinkin Duniya domin kafa gonakin noman rani masu inganci.
Ya yi nuni da cewa dogaro da noman damina kadai ba zai dore ba, saboda karuwar al’ummar yankin, wanda ala tilas sai an hada da noman rani.
Zulum ya kuma jaddada bukatar yin bincike kan amfanin gona masu jure yanayi don tabbatar da isasshen abinci da wadatar abinci ga al’ummar wannan yanki.
Ya ba da shawarar cewa, shirin noman ranin zai iya tallafa wa ci gaban kiwon dabbobi, yadda za a samu wadataccen nama da kuma nono a yankin.
A cewar gwamnan, “kafa manyan gonakin noman rani na buƙatar jajircewa daga gwamnoni da abokan tarayya da gwamnatocin kasashenmu don ganin mun cim ma manufar hakan a kan lokaci, yadda al’ummomin za su amfana”, in ji shi.
Ya kuma jaddada cewa, “gabar Tafkin Chadi na samar da wadataccen ruwa, kuma ana iya haka rijiyoyi da sanya bututun tura ruwa inda ruwan ya yi ƙaranci don al’ummar wuraren su amfana.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Noman rani
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Karamar Hukumar Bubura Ta Kai Tallafin Kayayyakin Abinci Cibiyar Gyaran Hali
Daga Usman Mohammed Zaria
Majalisar Ƙaramar Hukumar Babura ta Jihar Jigawa ta bayar da tallafin abinci ga fursunonin cibiyar gyaran hali ta Babura a matsayin wani ɓangare na ayyukan jin ƙai na majalisar.
Yayin ziyarar, Alhaji Hamisu Muhammad Garu ya bayyana cewa, wannan taimako ya biyo bayan lura da bukatun fursunonin yayin da ya kai ziyara ta duba cibiyar a baya.
A cewarsa, manufar bayar da tallafin ita ce don tallafa musu wajen kyautata rayuwarsu da kuma karfafa musu gwiwa su zama mutane nagari bayan sun fito daga gidan gyaran hali.
A nasa jawabin, jami’in da ke kula da cibiyar gyaran hali ta Babura, ASP Muhammad Ali, ya gode wa shugaban ƙaramar hukumar bisa wannan karamci, yana mai cewa taimakon ya zo ne a lokacin da ake matuƙar buƙata.
A yayin hudubarsa ga fursunonin, Babban Limamin Babura, Imam Salisu Aliyu, ya shawarce su da su nemi gafarar Allah, su kuma kara kusanci gare Shi, tare da rungumar canji mai kyau.
Kayan tallafin da aka bayar sun haɗa da buhunan masara, gero, shinkafa, garin rogo, man gyada, sinadaran dandano, gidan sauro da maganin kwari.
Manyan baƙin da suka raka shugaban ƙaramar hukumar a lokacin ziyarar sun haɗa da Hakimin Babura, Sarkin Bai Ringim, Alhaji Muhammad Nata’ala Mustapha, jami’in ‘yan sanda mai kula da yankin, CSP Abdu Jinjiri, da jami’in Hukumar Tsaro ta Civil Defence, CSC Sunusi Usman Chamo, da sauransu.