Noman rani ne zai kawar da yunwa a Yankin Tafkin Chadi — Zulum
Published: 12th, February 2025 GMT
Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum ya jaddada buƙatar samar da manyan gonakin gudanar da noman rani domin yaki da matsalar karancin abinci a Yankin Tafkin Chadi.
Gwamnan ya bayyana haka ne a yayin taron Gwamnonin Tafkin Chadi da aka gudanar makon da ya gabatar a garin Maiduguri fadar Jihar Borno karo na biyar, inda ya jadadda cewar, Allah SWT ya azurta wannan Yanki na Tafkin Chadi da dimbin filayen noma wanda idan aka yi amfani da su yadda ya kamata, na iya ba da gudummawa sosai wajen samar da abinci a yankin har ma da yankuna makwabta.
Zulum ya bayyana muhimmancin haɗin gwiwa tsakanin gwamnonin yankin da abokan haɗin gwiwa da Majalisar Dinkin Duniya domin kafa gonakin noman rani masu inganci.
Ya yi nuni da cewa dogaro da noman damina kadai ba zai dore ba, saboda karuwar al’ummar yankin, wanda ala tilas sai an hada da noman rani.
Zulum ya kuma jaddada bukatar yin bincike kan amfanin gona masu jure yanayi don tabbatar da isasshen abinci da wadatar abinci ga al’ummar wannan yanki.
Ya ba da shawarar cewa, shirin noman ranin zai iya tallafa wa ci gaban kiwon dabbobi, yadda za a samu wadataccen nama da kuma nono a yankin.
A cewar gwamnan, “kafa manyan gonakin noman rani na buƙatar jajircewa daga gwamnoni da abokan tarayya da gwamnatocin kasashenmu don ganin mun cim ma manufar hakan a kan lokaci, yadda al’ummomin za su amfana”, in ji shi.
Ya kuma jaddada cewa, “gabar Tafkin Chadi na samar da wadataccen ruwa, kuma ana iya haka rijiyoyi da sanya bututun tura ruwa inda ruwan ya yi ƙaranci don al’ummar wuraren su amfana.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Noman rani
এছাড়াও পড়ুন:
An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
Ƙungiyar Malaman Makarantu ta Najeriya (NUT) reshen Jihar Gombe, ta ziyarci shugaban ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomi na jihar, Barista Sani Ahmad Haruna, a ofishinsa da ke Gombe.
Shugaban ƙungiyar, wanda shi ne shugaban Ƙaramar Hukumar Gombe, ya bayyana cewa gwamnati da shugabannin ƙananan hukumomi za su ci gaba da yin duk mai yiwuwa wajen inganta walwalar malamai.
Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyiYa ce: “Ba za mu taɓa barin malamai su shiga cikin matsanancin hali ba. Za mu duba matsalolinsu domin tabbatar da walwalarsu da ci gaban ilimi a jihar.”
Sani, ya kuma yaba da yadda NUT ke tattaunawa cikin lumana da kawo shawarwari maimakon ɗaukar matakan da za su iya kawo tsaiko ga harkar ilimi.
A nasa jawabin, shugaban NUT na jihar ya ce sun kai ziyarar ne domin tattauna matsalolin da malamai ke fuskanta, musamman na makarantun firamare da ƙananun sakandare da ke ƙarƙashin kulawar ƙananan hukumomi.
Ya ƙara da cewa manufar NUT ita ce samar da fahimtar juna da haɗin kai tsakaninsu da shugabannin ƙananan hukumomi domin gano hanyoyin magance matsaloli cikin lumana.