A ci gaba da kokarinta na samun tagomashi a fannin tattalin arziki da ci gaban jihar ta hanyar kawo sauyi a harkar noma, gwamnatin jihar Jigawa na shirin hada gwiwa da wani kamfani da ke samar da dabino  da bayar da shawarwari a harkar noma, wanda ke da ofishi a Najeriya a kasar Saudiyya domin bunkasa noman dabino a jihar.

Gwamna Malam Umar Namadi ne ya bayyana hakan a yayin da ya karbi bakuncin wata tawaga daga daya daga cikin manyan kamfanonin noma na kasar Saudiyya, wadanda suka kware a harkar noman dabino da sarrafa gonaki, karkashin jagorancin Abdul’aziz Abdurrahman Al-Awf, wadanda suka kai masa ziyarar ban girma a gidan gwamnati dake Dutse.

Babban makasudin ziyarar ita ce tattaunawa kan dabarun hadin gwiwa da nufin bunkasa noman dabino a Jigawa, ta hanyar bunkasar fasahar noma, da musayar ra’ayoyi, da zuba jari a fannin noma.

Da yake jawabi a wajen taron, Abdul’aziz Al-Awf ya bayyana kudirin kamfaninsa na kawo sabbin dabarun noman zamani a jihar Jigawa, tare da tabbatar da samar da dabino a duk shekara maimakon noman rani, inda ya nuna cewa hadin gwiwar zai kunshi horar da manoma sosai, da karfafawa matasa gwiwa, da kuma bullo da wasu nau’o’in dabino masu kima da yawan amfanin gona a kasar Saudiyya.

“Wannan hadin gwiwa ba wai kawai zai kara yawan dabino da ake nomawa a Jigawa ba ne, har ma da inganta shi, wanda hakan zai sa jihar ta zama cibiyar noman dabino a Najeriya da Afrika,” inji shi.

Gwamna Namadi ya bayyana cikakken goyon bayan gwamnatinsa ga shirin, yana mai cewa ya yi daidai da tsarin bunkasa noma na jihar.

“Muna maraba da ku zuwa jihar Jigawa kuma mun yaba da sha’awar ku ta yin aiki da mu. A matsayinmu na gwamnati mun jajirce sosai wajen wannan hadin gwiwa domin zai amfani al’ummarmu matuka. Ziyarar ku da kuma shirye-shiryen ku na hadin gwiwa da mu kan samar da noman dabino a fadin jihar nan, tare da inganta noman alkama, sun yi dai dai da burinmu na bunkasa noma.”

Ya bayyana  Jigawa a matsayin kan gaba wajen noman alkama a Najeriya, tare da jaddada manufarsa ta fadada noman dabino a jihar.

Gwamna Namadi ya jaddada shirin gwamnatinsa na samar da duk wani abu da ake bukata domin ganin an samu nasarar aiwatar da aikin.

Ya kuma bayyana kwarin gwiwar cewa hadin gwiwar zai samar da fa’ida sosai, tare da sanya Jigawa a matsayin kan gaba a masana’antar dabino ta duniya.

“Mun himmatu wajen mai da jihar Jigawa cibiyar noman dabino, ba kawai don amfanin gida ba har ma da fitar da shi zuwa kasashen waje domin bunkasa tattalin arzikin jihar. 

A yayin ziyarar, tawagar  ta Saudiyya tare da wakilan kamfanin Netay Agro-Tech sun zagaya wurare daban-daban a fadin jihar domin tantance dabino da ake da su.

Abubakar Musa Bamai, Shugaban Kamfanin Netay Agro-Tech, ya bayyana dimbin ayyukan da aka riga aka yi, wadanda suka hada da nazarin kasa da tuntubar juna da cibiyoyin bincike.

Ya sanar da cewa nau’in dabino guda hudu da ake nema, wato Mejdool (Meju), Barhi (Bari), Sukkari (Sukari), da Ajwa—an bayyana su a matsayin wadanda suka dace don noma mai inganci a Jigawa.

 

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Saudiyya wadanda suka jihar Jigawa hadin gwiwa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa October 31, 2025 Manyan Labarai Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar October 31, 2025 Manyan Labarai NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
  • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida