Gwamnatin Jigawa Za Ta Hada Hannu Da Masana Harkar Dabino Na Kasar Saudiyya
Published: 12th, February 2025 GMT
A ci gaba da kokarinta na samun tagomashi a fannin tattalin arziki da ci gaban jihar ta hanyar kawo sauyi a harkar noma, gwamnatin jihar Jigawa na shirin hada gwiwa da wani kamfani da ke samar da dabino da bayar da shawarwari a harkar noma, wanda ke da ofishi a Najeriya a kasar Saudiyya domin bunkasa noman dabino a jihar.
Gwamna Malam Umar Namadi ne ya bayyana hakan a yayin da ya karbi bakuncin wata tawaga daga daya daga cikin manyan kamfanonin noma na kasar Saudiyya, wadanda suka kware a harkar noman dabino da sarrafa gonaki, karkashin jagorancin Abdul’aziz Abdurrahman Al-Awf, wadanda suka kai masa ziyarar ban girma a gidan gwamnati dake Dutse.
Babban makasudin ziyarar ita ce tattaunawa kan dabarun hadin gwiwa da nufin bunkasa noman dabino a Jigawa, ta hanyar bunkasar fasahar noma, da musayar ra’ayoyi, da zuba jari a fannin noma.
Da yake jawabi a wajen taron, Abdul’aziz Al-Awf ya bayyana kudirin kamfaninsa na kawo sabbin dabarun noman zamani a jihar Jigawa, tare da tabbatar da samar da dabino a duk shekara maimakon noman rani, inda ya nuna cewa hadin gwiwar zai kunshi horar da manoma sosai, da karfafawa matasa gwiwa, da kuma bullo da wasu nau’o’in dabino masu kima da yawan amfanin gona a kasar Saudiyya.
“Wannan hadin gwiwa ba wai kawai zai kara yawan dabino da ake nomawa a Jigawa ba ne, har ma da inganta shi, wanda hakan zai sa jihar ta zama cibiyar noman dabino a Najeriya da Afrika,” inji shi.
Gwamna Namadi ya bayyana cikakken goyon bayan gwamnatinsa ga shirin, yana mai cewa ya yi daidai da tsarin bunkasa noma na jihar.
“Muna maraba da ku zuwa jihar Jigawa kuma mun yaba da sha’awar ku ta yin aiki da mu. A matsayinmu na gwamnati mun jajirce sosai wajen wannan hadin gwiwa domin zai amfani al’ummarmu matuka. Ziyarar ku da kuma shirye-shiryen ku na hadin gwiwa da mu kan samar da noman dabino a fadin jihar nan, tare da inganta noman alkama, sun yi dai dai da burinmu na bunkasa noma.”
Ya bayyana Jigawa a matsayin kan gaba wajen noman alkama a Najeriya, tare da jaddada manufarsa ta fadada noman dabino a jihar.
Gwamna Namadi ya jaddada shirin gwamnatinsa na samar da duk wani abu da ake bukata domin ganin an samu nasarar aiwatar da aikin.
Ya kuma bayyana kwarin gwiwar cewa hadin gwiwar zai samar da fa’ida sosai, tare da sanya Jigawa a matsayin kan gaba a masana’antar dabino ta duniya.
“Mun himmatu wajen mai da jihar Jigawa cibiyar noman dabino, ba kawai don amfanin gida ba har ma da fitar da shi zuwa kasashen waje domin bunkasa tattalin arzikin jihar.
A yayin ziyarar, tawagar ta Saudiyya tare da wakilan kamfanin Netay Agro-Tech sun zagaya wurare daban-daban a fadin jihar domin tantance dabino da ake da su.
Abubakar Musa Bamai, Shugaban Kamfanin Netay Agro-Tech, ya bayyana dimbin ayyukan da aka riga aka yi, wadanda suka hada da nazarin kasa da tuntubar juna da cibiyoyin bincike.
Ya sanar da cewa nau’in dabino guda hudu da ake nema, wato Mejdool (Meju), Barhi (Bari), Sukkari (Sukari), da Ajwa—an bayyana su a matsayin wadanda suka dace don noma mai inganci a Jigawa.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Saudiyya wadanda suka jihar Jigawa hadin gwiwa
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka
Yayin taron manema labarai na yau Alhamis, kakakin ma’aikatar cinikayyar kasar Sin He Yongqian, ta ce ba su da wata masaniya, game da cewa shugaban Amurka na shirin jagorantar wata tawagar ‘yan kasuwa zuwa kasar Sin.
Sai dai kuma duk da hakan, a cewarta har kullum matsayar Sin a bayyane take, cewa tana fatan ita da Amurka za su bi turba guda, kuma karkashin jagorancin yarjejeniyoyin da shugabannin kasashen biyu suka amince da su, za su rungumi ka’idojin mutunta juna, da zama cikin lumana, da gudanar da hadin gwiwar cimma moriyar juna, ta yadda za a ci gaba da cimma matsaya guda.
Har ila yau, sassan biyu za su kai ga rage sabani, da karfafa hadin gwiwarsu, da bunkasa alakar tattalin arziki da cinikayya mai armashi da daidaito tsakanin kasashen biyu. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp