A yau Litinin, kasar Sin ta sanar da sabbin ka’idojin kyautata kare sirrikan jama’a yayin kare tsaron al’umma.

Firaministan kasar Sin Li Qiang ne ya rattaba hannu kan wata dokar majalisar gudanarwar kasar, domin fitar da ka’idojin, wadanda za su fara aiki daga ranar 1 ga watan Afrilu.

Ka’idojin na da nufin tafiyar da harkokin da suka shafi kula da tsare-tsaren kyamarorin da aka kafa domin tsaron al’umma da kare sirrika da hakkoki da muradu da ma bayanan daidaikun mutane.

(Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kwara Ta Kwashe Mabarata Daga Titunan Jihar Su 94

Gwamnatin jihar Kwara ta kori mabarata 94 daga titunan Ilorin, domin tantancewa, gurfanar da su da kuma mayar da su gida.

 

Da take magana da ‘yan jarida yayin aikin, kwamishiniyar jin dadin jama’a da ci gaban jihar Dr Mariam Nnafatima Imam ta ce wadanda aka kama domin dawo da su sun hada da mata 43 da maza 51.

 

Ta ce ma’aikatar ta yi aikin dawo da mabaratan domin an haramta barace-barace a jihar Kwara.

 

Imam ya godewa gwamnan jihar bisa kokarin da yake yi na ganin jihar ta kawar da barace-barace a kan tituna da sauran matsalolin zamantakewa .

 

Kwamishinan ta ce a ko da yaushe gwamnatin jihar tana tuntubar gwamnatocin jihohin masu bara a tituna kafin a mayar da su jihohinsu.

 

A nasa jawabin, mataimaki na musamman ga gwamnan jihar Kwara kan sha da fataucin miyagun kwayoyi, Haliru Mikail ya ce galibin mutanen da ke bayyana kansu a matsayin mabarata suna safarar kwayoyi.

 

Ya ce aikin dakile barace-barace a kan tituna zai ci gaba da kasancewa domin tabbatar da zaman lafiya a tsakanin al’umma.

 

A nasa bangaren, shugaban sashin da ba na kariya ba, rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen jihar Kwara Mista Adebayo Okunola ya bayyana cewa, an gudanar da aikin ne domin tsaftace jihar daga matsalolin zamantakewa yayin da wadanda aka kama tare da gurfanar da su a gaban kotun da ta dace za a hukunta su daidai da dokar jihar ta 2019.

 

Ya yi nuni da cewa hukumar da ke aikin za ta tabbatar da hukunta wadanda aka kama.

 

An gudanar da aikin ne a wasu yankuna da aka zaba a cikin birnin Ilorin da suka hada da Geri Alimi, Junction Tanke, Garage Offa, Garage Tipper da Zango, da dai sauransu.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NBRDA Za Ta Hada Gwiwa Da KIRCT Domin Habaka Magunguna Da Yaki Da Cututtuka
  • Afirka ta Kudu na shirin daukar matakan kauce wa tasirin harajin Amurka
  • Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta
  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Hukumar Kula da Da’ar Ma’aikata Za Ta Fara Daukar Bayanai Ta Yanar Gizo
  • Kwara Ta Kwashe Mabarata Daga Titunan Jihar Su 94
  • Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC
  • Mamakon ruwan sama ya haddasa ambaliya a Maiduguri 
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
  • Nijar da Rasha sun ƙulla yarjejeniyar makamashin nukiliya