Alkaluman Farashin Kayayyaki A Sin Sun Karu Zuwa Kaso 0.5 A Janairu
Published: 9th, February 2025 GMT
Alkaluman farashin kayayyakin masarufi na kasar Sin (CPI), wanda ke auna matakin hauhawar farashin kayayyakin, sun daga da kaso 0.5 bisa dari a watan Janairu.
Adadin ya karu ne kan kaso 0.1 bisa dari da ya kasance a baya, galibi saboda hutun bikin bazara na sabuwar shekarar gargajiya ta kasar Sin, a cewar hukumar kididdigar kasar.
এছাড়াও পড়ুন:
Tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa har zuwa baɗi — IMF
Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta hasashen cewa tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa tun daga shekarar nan ta 2025 har zuwa 2026.
IMF ya bayyana sabon hasashen a watan Yulin da muke ciki wanda a ciki ya yi ƙiyasin samun ƙarin bunƙasar tattalin arzikin Nijeriya.
Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasaAsusun ya yi hasashen samun ƙarin bunƙasar tattalin arzikin Nijeriya da kashi 3.4 a 2025, ƙari a kan hasashen kashi 3.0 da ya yi a watan Afrilu.
Haka kuma, IMF ya yi hasashen cewa tattalin arzikin Nijeriya zai samun ƙarin bunƙasa da kashi 3.2 a 2026, saɓanin hasashen kashi 2.7 da ya yi a watan na Afrilu.
Sai dai duk da wannan, wani rahoto IMF ya fitar a watan Yunin bana, ya ce Nijeriya na mataki na 12 a cikin jerin kasashe mafiya talauci a fadin duniya.
IMF ya ce talauci na kara karuwa a cikin kasar da ta dauki shekaru biyu tana kokarin sauya fuskar tattalin arziki, amma kuma take dada fadawa cikin duhu na tattalin arziki.
A cikin kasashe 189 da aka gudanar da bincike a cikinsu, Nijeriyar na a mataki na 178, inda ta zarta kasashe irin su Yemen da Sudan ta Kudu da Kwango da Nijar da Sudan, wadanda kusan dukkaninsu ke fama da rigingimu a halin yanzu.