Babbar Gasar Wasannin Kankara Ta Zama Damar Tabbatarwa Duniya Niyyar Karfafa Zaman Lafiya
Published: 9th, February 2025 GMT
A rana Juma’a da ta gabata, aka kaddamar da gasar wasannin kankara ta nahiyar Asiya karo na 9, a birnin Harbin na lardin Heilongjiang na kasar Sin. Wannan gasa ta kasance babbar gasar wasannin kankara ta kasa da kasa karo na 2 da Sin ta karbi bakuncinta, biyo bayan gasar wasannin Olympics na lokacin sanyi da ta gudana a birnin Beijing na Sin, a shekarar 2022.
Wata babbar ma’ana ta gasar ta wannan karo, ita ce tabbatar da hadin kan kasashen nahiyar Asiya. Ko da yake tattalin arzikin nahiyar na ta samun ci gaba cikin matukar sauri cikin shekaru 50 da suka gabata, sauyawar yanayin al’amuran siyasa na duniya, da takarar da ake yi tsakanin kasashe daban daban, suna ci gaba da haifar da kalubale a nahiyar. Bisa la’akari da wannan yanayin da ake ciki, taken gasar wasannin kankara ta nahiyar Asiya ta wannan karo na “tabbatar da hadin kan kasashen nahiyar Asiya” ya nuna bukatar dake akwai, gami da burin jama’ar kasashen Asiya na karfafa zaman lafiya da ci gaban tattalin arziki a kasashensu.
A wajen bikin kaddamar da gasar wasannin kankara ta wannan karo, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shawarwarin karfafa niyyar tabbatar da zaman lafiya, da ci gaban tattalin arziki, da cudanya, da kauna, tsakanin kasashen Asiya, gami da kasashen duk duniya baki daya, wadanda suka nuna yadda kasar Sin ke kokarin sauke nauyin dake wuyanta, na nemo wa duniya hanyar samun ci gaba mai dacewa, a matsayinta na wata babbar kasa. (Bello Wang)
কীওয়ার্ড: gasar wasannin kankara ta ta wannan karo nahiyar Asiya
এছাড়াও পড়ুন:
Pezeshkian: Iran da Masar suna da tsohon tarihi a duniya
Shugaban Jamhuriyar Musulunci ta Iran a wata ganawa da takwaransa na kasar Masar ya bayyana cewa: Iran da Masar sun mallaki wasu al’adu guda biyu masu cike da tarihi masu alfahari da fa’ida, kuma fadada hadin gwiwar da ke tsakaninsu zai kara taimakawa wajen tabbatar da moriyar al’ummomin kasashen biyu da ma sauran al’ummomin yankin.
Babban labarin jaridar Pars Today na cewa, Shugaban Jamhuriyar Musulunci ta Iran Masoud Pezeshkian a yau litinin a ci gaba da tarukan da yake yi a gefen taron gaggawa na kasashen musulmi da kungiyar hadin kan kasashen Larabawa a birnin Doha na kasar Qatar ya gana da shugaban kasar Masar Abdel Fattah el-Sisi. Da take bayyana fatan gaggauta kulla alaka a tsakanin kasashen biyu, Pezeshkian ta bayyana cewa: karfafa hadin kai da hadin kai tsakanin kasashen musulmi, ita ce hanya mafi inganci wajen dakile maimaitawa da ci gaba da laifukan gwamnatin Isra’ila.
El-Sisi, ya bayyana jin dadinsa da taron da kuma yadda dangantakar Iran da Masar ke ci gaba da bunkasa, ya jaddada cewa Tehran da Alkahira na da karfin da za su iya tabbatar da moriyar juna da kuma moriyar sauran kasashen yankin. Haka nan kuma ya jaddada muhimmancin kusanci tsakanin kasashen musulmi da kuma daukar matsaya daya a aikace kan laifukan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila.
Tashar talabijin ta 13 ta gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila, wadda ta yi tsokaci kan rikicin siyasa da diflomasiyya na Isra’ila bayan harin da aka kai a birnin Doha, ya bayar da rahoton cewa, Isra’ila na kara zama saniyar ware a fagen kasa da kasa, yayin da Masar, Saudiyya, da Jordan ke kara kusantar Iran. Tashar ta bayyana halin da Isra’ila ke ciki a halin yanzu a matsayin tsunami na siyasa, inda ta kara da cewa warewar Isra’ila a duniya na karuwa kuma kasashen da a da suke daukar kansu aminan Tel Aviv – irin su Saudiyya, Masar, da Jordan – a yanzu suna karfafa alaka da Iran.
Masoud Kazemian wani mai sharhi kan al’amuran yammacin Asiya ya rubuta game da kulla cikakkiyar alaka tsakanin Iran da Masar, inda ya bayyana cewa dangantaka tsakanin Tehran da Alkahira ta zama wata muhimmiyar bukata. Ya yi nuni da cewa, wannan kusanci ba wai kawai yana amfanar tsaron kasa da tattalin arzikin kasashen biyu ba ne, har ma zai iya ba da gudummawa wajen samar da kwanciyar hankali da kwanciyar hankali.
Masanin siyasar ya jaddada cewa, ta fuskar jami’an diflomasiyyar Iran da na Masar, hadin gwiwar da ke tsakanin Tehran da Alkahira na iya zama “sabuwar yanayin kwanciyar hankali” da kuma taimakawa wajen daidaitawa da kawancen kasashen Yamma da sahyoniya.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran ta samu Zinariya, Azurfa, da Tagulla a Gasar Kokawa ta Duniya September 18, 2025 Iran Ta Yi Nasarar Gwajin Tauraron Dan’adam Da Zai Samar Da “Internet” Ga Yankunan Karkara September 17, 2025 Za A Kada Kuri’ar Raba Gardama Akan Sabon Tsarin Mulki A Kasar Guinea September 17, 2025 Larijani: Iran Da Saudiyya Za Su Bunkasa Aiki Tare A Fagagen Kasuwanci Da Tsaro September 17, 2025 Hukumar Tarayyar Turai Ta Gabatar Da Shawarar Jingine Aiki Da Yarjejeniyar Kasuwanci Da HKI September 17, 2025 Gaza: HKI Tana Ci Gaba Da Yi Wa Falasdinawa Kisan Kiyashi A Gaza September 17, 2025 Ma’aikatar Shari’ar Iran Ta Sanar Da Rataye Dan Leken Asirin Hukumar Mossad Ta Isra’ila September 17, 2025 Hamas Ta Zargi HKI Da Shirga Karya Don Kare Muggan Manufofinta September 17, 2025 Iran Ta Bayyana Abubuwan Da Bata Amince Da Su Ba A Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar OIC A Birnin Doha September 17, 2025 Chadi: Majalisa ta amince a baiwa shugaban kasa damar ci gaba da Mulki har karshen rayuwa September 17, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci