A rana Juma’a da ta gabata, aka kaddamar da gasar wasannin kankara ta nahiyar Asiya karo na 9, a birnin Harbin na lardin Heilongjiang na kasar Sin. Wannan gasa ta kasance babbar gasar wasannin kankara ta kasa da kasa karo na 2 da Sin ta karbi bakuncinta, biyo bayan gasar wasannin Olympics na lokacin sanyi da ta gudana a birnin Beijing na Sin, a shekarar 2022.

An ce, gasar wasannin kankara ta wannan karo ta samu halartar ‘yan wasa fiye da 1270 da suka zo daga kasashe da yankuna 34 dake nahiyar Asiya, alkaluman da suka kai matsayin koli a tarihi. Inda har wasu kasashen da ba sa samun yanayi mai sanyi da muhalli mai kankara a cikin gida, kamarsu UAE, da Vietnam, da Indonesia, da Thailand, da dai sauransu, su ma suka tura tawagogi su halarci gasar.

Wata babbar ma’ana ta gasar ta wannan karo, ita ce tabbatar da hadin kan kasashen nahiyar Asiya. Ko da yake tattalin arzikin nahiyar na ta samun ci gaba cikin matukar sauri cikin shekaru 50 da suka gabata, sauyawar yanayin al’amuran siyasa na duniya, da takarar da ake yi tsakanin kasashe daban daban, suna ci gaba da haifar da kalubale a nahiyar. Bisa la’akari da wannan yanayin da ake ciki, taken gasar wasannin kankara ta nahiyar Asiya ta wannan karo na “tabbatar da hadin kan kasashen nahiyar Asiya” ya nuna bukatar dake akwai, gami da burin jama’ar kasashen Asiya na karfafa zaman lafiya da ci gaban tattalin arziki a kasashensu.

A wajen bikin kaddamar da gasar wasannin kankara ta wannan karo, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shawarwarin karfafa niyyar tabbatar da zaman lafiya, da ci gaban tattalin arziki, da cudanya, da kauna, tsakanin kasashen Asiya, gami da kasashen duk duniya baki daya, wadanda suka nuna yadda kasar Sin ke kokarin sauke nauyin dake wuyanta, na nemo wa duniya hanyar samun ci gaba mai dacewa, a matsayinta na wata babbar kasa. (Bello Wang)

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: gasar wasannin kankara ta ta wannan karo nahiyar Asiya

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Ivory Coast Ya Bayyana Shirinsa Na Sake Tsayawa Takarar Shugabanci Karo Na Hudu

Shugaban kasar Ivory Coast Alhassan Outtara ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugabancin kasar a karo na 4 wanda za a gudanar a watan Oktoba mai zuwa.

Za a yi manyan zabukan kasar ta Ivory Coast ne dai a ranar 25 ga watan na Oktoba mai zuwa.

Shi dai Alassan Outtara an sake zabarsa shugaban kasa karo na uku  a 2020, alhali tun a baya ya sanar da cewa zai sauka daga kan mukamin nashi.

Outtara ya zama shugaban kasar ta Ivory Coast a karon farko a 2010 a kasar da ita ce mafi girma wajen fitar da Coco a duniya.

Kamfanin dillancin labarun “Reuters’ ya amabto Ottata yana cewa: “Tsarin mulkin kasarmu ya ba ni damar in sake yin hidima a wani jikon, kuma inda da cikakkiyar lafiyar da za ta sa in yi hakan.”

Haka nan kuma ya ce; Ina sake tsaywa takara saboda kasarmu tana fuskantar kalubale mai girma a fagagen tattalin arziki da tsaro da ba a tsaba fuskantar irinsa ba a baya.

 Gabanin zamansa shugaban kasa, Outtara ya kasance kwararre a fagen tattalin arziki wanda ya yi karatunsa a kasar Amurka. Daga cikin ayyukan da ya yi da akwai gwamnan Bankin yammacin Afirka, sannan kuma mataimakin shugaban Asusun Bayar da Lamuni Na Duniya ( IMF).

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu July 30, 2025 MDD Zata Aiwatar Da Hanyar Warware Rikicin Falasdinawa Da Yahudawan Sahayoniyya July 30, 2025 Birtaniya Ta Yi Barazanar Amincewa Da Kasar Falasdinu A Watan Satumba Idan Yanayin Gaza Bai Canza Ba July 30, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Lod Da Ke Jaffa Da Makami Mai Linzami July 30, 2025 Faransa Ta Bayyana Wuce Gona Da Irin ‘Yan Sahayoniyya Kan Falasdinawa Da Ayyukan Ta’addanci July 30, 2025 Jagora: Iran Ta Bayyana Karfinta Da Jajircewarta A Yakin Kwanaki 12 Ga Duniya July 29, 2025 Mutum daya Yayi Shahada 4 Sun Ji Rauna Sanadiyar Hare-Haren HKI A Lebanon July 29, 2025 EU Tace Zata Dakatar Da HKI Daga Cibiyar Bincikenta Saboda Gaza July 29, 2025 Ma’aikatar Leken Asirin JMI Ta Ce Ta Gano Shirin Kashe Manyan Mutane 35 a kasar July 29, 2025 Najeriya: Likitoci a Lagas Sun Shiga Yajin Aiki July 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka
  • Kananan Yan Wasan Dabben Gargajiya Na Iran Sun Zama Zakara A Gasar Wannan Shekara
  • Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila
  • Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki
  • Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United
  • Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya
  • Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka
  • Shugaban Kasar Ivory Coast Ya Bayyana Shirinsa Na Sake Tsayawa Takarar Shugabanci Karo Na Hudu
  • Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa
  • Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON