OIC Ta Yi Allawadai Da Furucin Shugaban Kasar Amurka Akan Gaza
Published: 9th, February 2025 GMT
Kungiyar kasashen musulmi ( OIC) ta fitar da bayani da aciki ta yi tir da maganganun shugaban kasar Amurka Donald Trump akan fitar da mutanen Gaza.
Kungiyar ta OIC ta bayyana cewa; maganganun na shugaban kasar Amurka suna a matsayin goyon bayan ‘yan mamaya, masu mulkin mallaka domin kwace kasar Falasdinawa da hakan yake a matsayin take dokokin kasa da kasa da kudurorin MDD da su ka hada da kwamitin tsaro na wannan Majalisar mai lamba;2334.
Haka nan kuma bayanin na kungiyar kasashen musulmin ya ce, abinda Trump ya furta zai iya hana zaman lafiya wanzuwa a cikin wannan yankin.
Wani sashe na kungiyar kasashen musulmin ya bayyana kin amincewa da duk wani yunkuri na sauya tsarin iyaka da mutane a Falasdinu, tare da yin kira da a tsagaita wutar yaki mai dorewa.
Haka nan kuma kungiyar ta OIC ta nuna cikakken goyon bayanta ga hukumar Agaji ta Falasdinawa ta “UNRWA” wacce Isra’ila da Amurka su ka haramtawa kansu aiki da ita.
Kungiyar ta kuma nuna cikakken goyon bayanta ga al’ummar Falasdinu da kuma fadi tashin da suke yi na samun ‘yanci a karkashin kungiyar PLO.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Ivory Coast Ya Bayyana Shirinsa Na Sake Tsayawa Takarar Shugabanci Karo Na Hudu
Shugaban kasar Ivory Coast Alhassan Outtara ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugabancin kasar a karo na 4 wanda za a gudanar a watan Oktoba mai zuwa.
Za a yi manyan zabukan kasar ta Ivory Coast ne dai a ranar 25 ga watan na Oktoba mai zuwa.
Shi dai Alassan Outtara an sake zabarsa shugaban kasa karo na uku a 2020, alhali tun a baya ya sanar da cewa zai sauka daga kan mukamin nashi.
Outtara ya zama shugaban kasar ta Ivory Coast a karon farko a 2010 a kasar da ita ce mafi girma wajen fitar da Coco a duniya.
Kamfanin dillancin labarun “Reuters’ ya amabto Ottata yana cewa: “Tsarin mulkin kasarmu ya ba ni damar in sake yin hidima a wani jikon, kuma inda da cikakkiyar lafiyar da za ta sa in yi hakan.”
Haka nan kuma ya ce; Ina sake tsaywa takara saboda kasarmu tana fuskantar kalubale mai girma a fagagen tattalin arziki da tsaro da ba a tsaba fuskantar irinsa ba a baya.
Gabanin zamansa shugaban kasa, Outtara ya kasance kwararre a fagen tattalin arziki wanda ya yi karatunsa a kasar Amurka. Daga cikin ayyukan da ya yi da akwai gwamnan Bankin yammacin Afirka, sannan kuma mataimakin shugaban Asusun Bayar da Lamuni Na Duniya ( IMF).
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu July 30, 2025 MDD Zata Aiwatar Da Hanyar Warware Rikicin Falasdinawa Da Yahudawan Sahayoniyya July 30, 2025 Birtaniya Ta Yi Barazanar Amincewa Da Kasar Falasdinu A Watan Satumba Idan Yanayin Gaza Bai Canza Ba July 30, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Lod Da Ke Jaffa Da Makami Mai Linzami July 30, 2025 Faransa Ta Bayyana Wuce Gona Da Irin ‘Yan Sahayoniyya Kan Falasdinawa Da Ayyukan Ta’addanci July 30, 2025 Jagora: Iran Ta Bayyana Karfinta Da Jajircewarta A Yakin Kwanaki 12 Ga Duniya July 29, 2025 Mutum daya Yayi Shahada 4 Sun Ji Rauna Sanadiyar Hare-Haren HKI A Lebanon July 29, 2025 EU Tace Zata Dakatar Da HKI Daga Cibiyar Bincikenta Saboda Gaza July 29, 2025 Ma’aikatar Leken Asirin JMI Ta Ce Ta Gano Shirin Kashe Manyan Mutane 35 a kasar July 29, 2025 Najeriya: Likitoci a Lagas Sun Shiga Yajin Aiki July 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci