Hamas : Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Da Isra’ila Na Cikin Hadari”
Published: 9th, February 2025 GMT
Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta bayyana cewa yarjejeniyar tsagaita bude wuta tsakaninta da Isra’ila “tana cikin hadari” kuma “zata iya rugujewa,”
Bassem Naïm, ne wani mamba a ofishin siyasa na kungiyar, ya bayyana hakan ga kamfanin AFP, yayin da tattaunawar da ake yi kan mataki na biyu na tsagaita bude wuta, da ya kamata a fara ranar Litinin, ke ja da baya ba kamar yadda aka fara ba inji shi.
Da yake zargin Isra’ila da “jinkiri” wajen aiwatar da kashi na farko na yarjejeniyar tsagaita bude wuta na makonni shida, wanda ya fara aiki a ranar 19 ga watan Janairu, Bassem Naim ya yi gargadin cewa wannan lamarin ya jefa yarjejeniyar cikin hadari kuma zata iya haifar da rugujewarta.
Kawo yanzu dai ba a bayar da cikakken bayani kan ci gaban tattaunawar da ake yi a mataki na biyu ba, da nufin ganin an sako dukkan mutanen da aka yi garkuwa da su, da kuma kawo karshen yakin.
Isra’ila za ta saki fursunonin Falasdinawa 183 yau Asabar, a madadin wasu mutanenta uku daga cikin wadanda kungiyar Hamas ke garkuwa da su a Gaza a wani bangare na aiwatar da yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza da suka cimma.
Tun bayan fara tsagaita wutar, an sako wadanda ake garkuwa dasu 18 da da fursunonin falasdinawa 582.
Kashi na farko na yarjejeniyar, wanda zai dauki tsawon makonni shida, ya tanadi mikawa Isra’ila jimillar mutane 33 da aka yi garkuwa da su, ciki har da akalla takwas da suka mutu, a madadin Falasdinawa 1,900.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: yarjejeniyar tsagaita bude wuta
এছাড়াও পড়ুন:
Falasdinawa Da Dama Sun Yi Shahada A Zirin Gaza
Sojojin HKI suna ci gaba da kai hare-hare a sassa daban-daban na yankin zirin Gaza da su ka hada da sansanonin ‘yan hijira da kuma rusa gidajen da su ka saura a tsaye.
Tashar talabijin din ‘almayadin” ta bayyana cewa; An sami shahidai 7 da safiyar yau Laraba, bayan harin da ‘yan sahayoniyar su ka kai akan wani gida da yake a Deir-Balah,dake tsakiyar zirin Gaza.
A can sansanin ‘yan hijira dake kusa da filin wasa na ‘al-Anan’ kuwa mutane 4 ne su ka jikkata.
A yankin Safdawi dake cikin birnin Gaza, jiragen yakin HKI sun kai hare-hare akan wani gida wanda ya haddasa gobara, da kuma shahadar mutane 8.
A unguwar “Shuja’iyya” sojojin na mamaya sun rushe gidaje da dama.
Gabanin wannan lokacin, an sami wasu shahidan 3 da kuma jikkatar mutane 46 a kusa da cibiyar da Amurka da Isra’ila su ka ware domin raba kayan abinci.
Kididdiga ta karshe wacce ma’aikatar kiwon lafiya ta Gaza ta fitar ta bayyana cewa; adadin Falasdinawan da su ka yi shahada daga 7 ga Oktoba, sun kai dubu 45,56, sai kuma wadanda su ka jikkata da sun kai 129, da kuma 123.