Watanni 2 Da Sauke Baffa Bichi, An Nada Umar Farouk Mukamin Sakataren Gwamnatin Kano
Published: 9th, February 2025 GMT
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya nada Umar Farouk Ibrahim a matsayin sabon Sakataren Gwamnatin Kano.
Nadin na kunshe cikin wata sanarwar da Kakakin Gwamnatin Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya wallafa a shafukansa na sada zumunta a yammacin ranar Asabar 08, ga Febarairun 2025.
Dalilan Da Suka Sa Gwamnan Kano Sallamar SSG Da Wasu Kwamishinoni 5 Gwamnan Kano Ya Karyata Jita-jitar Rikicinsa Da Sakataren Gwamnatin JiharNadin Na Ibrahim zai fara aiki ne daga ranar Litinin mai zuwa 10, ga Febarairun 2025.
Sanarwar nadin ta bayyana cewa an zabi, Ibrahim a matsayin sabon Sakataren Gwamnatin Jihar saboda shafe sama da shekaru talatin ya na aikin gwamnati da tarin kwarewar aiki da yake da ita a hukumomi da ma’aikatu daban-daban na gwamnati da ya yi aiki, don cimma muradin gwamnati mai ci na ciyar da jihar Kano gaba.
Nadin na Umar Farouk Ibrahim, na zuwa ne watanni biyu bayan sauke tsohon Sakataren Gwamnatin Kano, Dr. Baffa Abdullahi Bichi daga muƙaminsa a sakamakon dalilan rashin lafiya, kamar yadda sanarwar sauke shi ta bayyana haka a baya. Sai dai duk da haka wasu na ganin kamar akwai wasu dalilai na siyasa saɓanin wanda aka bayyana na sauke Baffa Bichin.
কীওয়ার্ড: Gwamnan Kano Sakataren Gwamnatin Kano Umar Farouk Ibrahim Sakataren Gwamnatin Gwamnatin Kano
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Zamfara ta amince da naɗin sabon Sarkin Katsinan Gusau
Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naɗin Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello a matsayin sabon Sarkin Katsinan Gusau.
Sakataren Gwamnatin Zamfara, Malam Abubakar Mohammad Nakwada ne ya bayyana haka a wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Suleman Ahmad Tudu ya fitar a Talatar nan.
Ambaliya ta yi ajalin mutum 30 a China ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a AlkaleriSanarwar ta ce an yi amfani da dokoki da tanade-tanaden doka ne wajen amincewa da naɗin wanda masu zaɓen sarkin masarautar suka zaɓa.
Gwamna Lawal ya taya sabon sarkin murna, sannan ya yi kira gare shi da ya yi koyi da magabatansa, musamman ganin shi tsatson Malam Sambo Ɗan Ashafa ne.
Ya kuma yi kira ga sabon sarki ya dage wajen kira da samun haɗin kai da ci gaban masarautar Gusau da jihar, da ma ƙasar baki ɗaya.
Alhaji Abdulkadir zai ɗare karagar ne a matsayin Sarki na 16 na masarautar, inda zai maye gurbin mahaifinsa, Marigayi Mai martaba Dr. Ibrahim Bello, wanda ya rasu a ranar 25 ga watan Yulin 2025.
Sabon sarkin ne babban ɗan marigayin, kuma kafin naɗa shi sarki, shi ne Bunun Gusau.
Ana iya tuna cewa, a Juma’ar makon jiya ce aka samu rahoton rasuwar Sarkin Katsinan Gusau, Dokta Ibrahim Bello yana da shekara 71 da haihuwa.
Sarkin ya rasu ne a daren Juma’a 24 ga watan Yulin 2025 bayan doguwar jinya a wani asibiti da ke Abuja, babban birnin Nijeriya.
Sanarwar da gwamnatin Zamfarar ta fitar ta ce: “Rasuwar mai martaba babban rashi ne ga Jihar Zamfara da ma daukacin Arewacin Nijeriya.”
Gwamna Dauda Lawal ne ya jagoranci jana’izar sarkin a Babban Masallacin Juma’a na Kanwuri da ke birnin Gusau.
A watan Maris na 2015 aka naɗa marigayi Dokta Ibrahim Bello a matsayin sarkin Gusau na 15, inda ya maye gurbin ɗan’uwansa Alhaji Muhammad Kabiru Danbaba bayan rasuwarsa.
Marigayin ya bar mata da ’ya’ya sama da 20.