Aminiya:
2025-11-02@16:59:20 GMT

Yadda Kano ke samar da madarar Naira biliyan 2.2

Published: 8th, February 2025 GMT

Madara muhimmin abinci ne da ake bukata domin samun sinadarai masu ginawa da ƙara ƙarfi da lafiyar jiki.

Bincike ya nuna cewa mutane biliyan shida ne ke shan madara a duniya, wanda ya sa shan madarar saniya da kiwon dabbobi ya zama wani vangare na rayuwar ɗan adam.

Dubban mata Fulani suna samun kuɗaɗen shiga ta hanyar sayar da madara ga ɗaiɗaikun mutane ko jama’a ko ’yan kasuwa, waɗanda suke sha ko sarrafa shi domin amfanin kasuwanci.

Lura da muhimmancin madara ga rayuwar ɗan Adam da kuma ƙoƙarin rage haɗarin da ke tattare da shan ta, Hukumar Haɓaka Noma da Kiwon Dabbobi ta Jihar Kano (KSADP) ta zuba jarin Dala miliyan 8.03 don gina cibiyoyi 100 na tattara madara a jihar, da nufin tallafa wa makiyaya domin su wadatar da buƙatun masana’antar madara da sauran masu buqatar ta.

An tallafa wa Ƙungiyar Masu Sayar da Madarar Saniya ta Kasuwar Ƙofar Wambai da ɗakin ajiye kayan sanyi domin tabbatar da tsafta da kuma ingancin madara.

An kashe ɗan banga da yin garkuwa da ’yan mata 6 a Neja An dakatar da dagaci kan zargin saran maraya da adda

Shugaban ƙungiyarsu, Alhaji Muhammad Alaramma, ya ce harkar kiwon dabbobi na bunqasa sosai a Jihar Kano sakamakon matakin da gwamnatin jihar ta ɗauka ta hanyar hukumar KSADP, wadda ta ba wa ƙungiyar tallafin wurin ajiye kayan sanyi.

Lita dubu hamsin a kullum

“Kullum ana sayar da aqalla lita 50,000 na madara, amma wani lokaci ba ya kaiwa haka, saboda qarancin madara a Kano a halin yanzu. Mutane sukan kawo shi daga Jos da Bauchi da Jama’are da sauran wurare.

“Wurin ajiyar kayan sanyi da aka ba mu yana da matuqar amfani, amma ƙalubalen shi ne ba ya amfani da lantarki mai amfani da hasken rana. Amma mun yi yarjejeniya da wani wanda ya karɓi hayar wani vangare na wajen, shi kuma a madadin haka yana ba mu wutar lantarki, daga injin ɗinsa.

“Naira 200 muke karva a kan kowane bokitin madara da aka kawo ajiya daga hannun ’ya’yan qungiyarmu, waɗanda sun kusa mutum 20,000,” in ji shugaban ga wakilinmu.

Barazanar ƙwayar cuta

Madarar da aka sarrafa na iya harbuwa da ƙwayar cuta idan ba a kiyaye ta ba, wanda hakan na iya shafar lafiyar ɗan Adam. Masana sun bayyana cewa kashi 70 cikin 100 na cututtukan da ke damun xan adam suna da alaƙa da dabbobi. Don haka shan madara mara tsafta na iya zama babban haxari ga lafiyar ɗan Adam.

Shirin Haɓaka Noma da Kiwon Dabbobi na Jihar Kano, tare da tallafin Bankin Ci-gaban Islama (IsDB) da Asusun Inganta Rayuwa (LLF), na gina cibiyoyi 100 na tattara madara a Kano don inganta samuwar madara domin kasuwanci da ɗaga darajarta, da kuma magance matsalar qarancinta da rashin ingancinta a harkar kasunwancin.

Wani ƙwararre kan kiwon dabbobi a KSADP, Dakta Garba Saleh, ya bayyana cewa ana gina cibiyoyin madarar ne domin tattara ta daga makiyaya domin a ci gaba da raba wa masu sarrafawa.

“Manufar ita ce tabbatar da tsafta da ingancin madara, ta yadda duk sinadaran da suka dace ba za a lalata su ba. Idan babu cibiyar tarawa za a iya rasa mahimman sinadaran da ke cikin madara cikin sauƙi.

“A ƙarƙashin shirin, za a kafa cibiyoyin tattara madara (MCC) guda 100 inda a halin yanzu an kammala 40 daga ciki.”

Yawa da darajar madarar

Ƙwararrun a fannin kiwon dabbobi ya bayyana cewa ana sa ran kowace cibiyar za ta ajiye aƙalla lita 28,000 na madara a mako, kimanin lita miliyan 1.46 a kowace shekara. Hakan nan nufin yawan dararar cibiyoyin guda 100 za su adana a shekara ya kai lita miliyan 146.

Ana kuma sa ran makiyaya 25 za su riƙa ba wa kowane MCC madara, ta yadda kowane MCC zai riƙa samar da Naira 4,622,872 a duk mako.

A wata guda zai samar da kimanin Naira miliyan 18.5, wato Naira miliyan 221 a duk wata. Hakan na nufin za a samu jimillar Naira biliyan 2.2 (Dala miliyan 1.4) daga MCC 100 ɗin a shekara.

Yadda cibiyoyin suke

Kowace cibiya tana amfani da wutar lantarki mai amfani hasken rana kuma tankin sanyaya abubuwa wanda aka qera da qarfe mara yin tsantsa; da kuma injin tata da famfo da na’urar xumama ruwa da kayan gwajin madara da na tsaftar muhalli da mazuban tattara madara da rijiyoyin burtsatse masu tankin sama.

Zuwa yanzu, an gina cibiyoyi biyar a Doguwa, huɗu a Albasu, huɗu a Danbatta, sannan uku-uku a Dansoshiya a Ƙaramar Hukumar Kiru da Garko da Garun Malam da Tofa da Kura da Dawakin Tofa.

Makiyaya na murna

Wani Bafulatani makiyayi a ƙauyen Ɗansoshiya, Muhammad Major, ya ce duk da cewa an an kammala cibiyar tara madarar yankinsu, amma dai ba ta fara aiki ba, amma duk da haka makiyaya suna farin ciki da kafa cibiyar.

Muhammad Major ɗan shekara 52 ya ce, “An kammala cibiyar Ɗansoshiya amma ba ta fara aiki ba, don haka Kano muke kai madara mu sayar. Amma idan ya fara aiki, nan zan riƙa kaiwa a ba ni kuɗina ba sai na kashe kuɗin mota zuwa Kano ba, ka ga na rage kashe kuɗi.”

Manyan kanfanoni irin su L&Z sukan yi amfani da cibiyoyin da KSADP ta kafa baya ga nasu na ƙashin kansu, ci-gaban kasuwancinsu.

Barazanar manyan kamfanoni

Wasu da ke harkar kuma sukan yi amfani da madarar gari ko waken suya, domin haɗawa da madarar shanun da suka samu daga masu kawo musu, wadda ta yi karancin sosai.

Wata Bafulatana da ke kawo nono Kano daga Bunkure, Hauwa’u Abubakar, ta ce ba a kafa irin wannan cibiya a yankinsu ba. Hauwa’u takan kashe kuɗin mota N1,000 a kullum zuwa Kano inda take sayar da bokiti uku zuwa biyar na nono kowanne a kan kimanin N6,5000, a duk tafiya.

Hauwa ta ce, “Kullum nan (Kano Line) nake kawo bokiti uku zuwa biyar na nono, inda muke sayar da duk bokiti a kan N6,500. Wasu a nan suke saya su kai Kasuwar Ƙofar Wambai su sake sayarwa, amma na fi so in tsaya a nan a saboda in rage kashe kuxin abin hawa.”

Shi ko Abdulmuɗɗalibi Sani, wanda ke sana’ar fura da nono, yakan sayi nono ne a wurin matan Fulani a cibiyar da ke Kano Line. Ya ce ya sayi bokiti shida saboda ya ya fi arha idan aka kwatanta da na Kofar Wambai, inda dillalai kan yi amfani da damar su ƙara farashi.

Ya ce ƙananan masu sayen nono irinsa na fama da manyan kamfanoni irin su L&Z da ke harkar, waxanda suke da nasu cibiyoyin tattara madara inda suke saya kai-tsaye daga hannun makiyaya.

Abdulmuɗɗalibi ya ce “Manyan mutane da ke saya kai-tsaye daga wurin matan Fulani su ke haddasa ƙarancin madara da tsadarsa, amma kuɗinsa bai kai haka ba.”

Wai mai sayar da madara, Awwal Sa’id wanda yakan sayi bokiti biyar zuwa shida a Kano Line ya ce, abin da ya jawo shi shi ne cinkoson da ke Ƙofar Wambai da kuma yadda dillalai ke sanya farashi.

Yadda za a bunƙasa harkar

Wani qwararre a fannin kiwon dabbobi a Hukumar KSADP, Dakta Garba Saleh, ya yi imanin cewa kasuwancin madara zai samu ci-gaba sosai a nan gaba.

Ya bayyana cewa ko da yake a halin yanzu Nijeriya ba ta samar da madarar da za ta wadatar da buqatar cikin gida, za a kai lokacin da qasar za ta riƙa fitar da ita zuwa ƙetare idan aka haɓaka tare da tallafa wa harkar.

Ya ce ƙasashen Kenya da Uganda da Rwanda sun bunƙasa fannin madararsu ne ta hanyar taimako da tallafa wa ƙananan kamfanoni domin fitar da ita zuwa qasashen qetare.

Qalubalen harkar

Sai dai kuma shanu ’yan qasa na daga cikin ƙalubalen. Dakta Saleh ya bayyana cewa shanu ’yan qasa ba sa samar da madara mai yawa, domin abin da suke samarwar a yini guda bai fi lita uku zuwa biyar ba, idan aka kwatanta da shanun qasashen waje da ke ba da lita 50 a kullum.

Sannan kuma ciyawa ’yar ƙasa ba ta da sinadaran gina jiki sosai, sannan yin kiwo ba tare da gandun kiwo ba, babu riba.

Ya ce domin magance wannan matsala Hukumar KSADP tana aiki a wani fili mai fafin hekta 3,000 inda za a noma nau’ika daban-daban na ciyayi da aka ƙara wa inganci, irin su nau’in Nafia da Stylo da kuma Gamba.

Hukumar KSADP na kuma aikin yin barbarar shanu ’yan qasa da na waje domin ganin sun samu siffofi da nagartar ’yan ƙasar waje.

Kafa Ma’aikatar Kiwon Dabbobi zai iya kawo sauyi ta hanyar samar da ingantaccen abincin dabbobi wanda zai inganta samar da madara mai nagarta da yawan gaske wanda hakan zai kawo riba mai tsoka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: madara ya bayyana cewa samar da madara Ya bayyana cewa tattara madara Hukumar KSADP

এছাড়াও পড়ুন:

Jerin Gwarazan Taurarinmu

3. A Hangen Nesansa wajen jagorancin al’umma, ya mayar da hankali kan masana’antu, sabunta ababen more rayuwa da kuma gina Dan’adam; domin mayar da Jihar Nasarawa matsayin wata babbar cibiyar zuba jari a Nijeriya da horar da aikin injiniya tare da kyautata jin dadin al’ummar jihar; an zabi Injiniya Abdullahi A. Sule a matsayin Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025.

Injiniya Abdullahi Sule: Wanda Ya Fi Yin Fice Kan Harkokin Masana’antu A Duk Fadin Arewa

4. Shugabancinsa ya yi matukar kawo sauye-sauye a Jihar Ekiti, musamman ta hanyar gudanar da mulki na adalci, sabunta ayyukan more rayuwa, karfafa matasa da fadada aikin gona; sakamakon tawali’un da yake da shi da horon da ya samu wajen tafiyar harkokin kudi da gina jama’a tare kuma karfafa al’adun demokuradiyya; ya sa aka zabi Biodun Abayomi Oyebanji a matsayin Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025.

Biodun Abayomi Oyebanji: Wanda Ya Kawo Juyin-juya-hali A Jihar Ekiti

5. A sauyin da ya kawo a shugabancinsa, jajircewarsa na kawo ci gaba a fannin tsaro, zuba jari mai yawan gaske a fannin ilimi, kiwon lafiya da sauran ababen more rayuwa; kazalika a kokarinsa na sake mayar da Jihar Zamfara kan turbar zaman lafiya da ci gaba mai dorewa, Dauda Lawal shi ne Gwarzon Gwamnanmu na wannan shekara.

Dauda Lawal: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba

6. Ya dukufa wajen mayar da hankali kan manufar da ya sanya gaba, mai taken; “MORE Agenda”, wanda ya sake fasalin tsarin mulkin Jihar Delta ta hanyar zaman lafiya, hadin kai da kuma jajircewa wajen samar da ababen more rayuwa, ilimi, lafiya da kuma gina al’adun jama’a bisa gaskiya, tsantseni a sha’anin harkar kudi ta bangarori da dama; Rt. Hon. Sheriff Oborebwori, shi ne gwarzon gwamnanmu na 2025.

Sheriff Oborebwori: Gwamnan Da Ya Ginu Kan Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Al’umma

7. Saboda kasancewarsa mai sasanta mutane da hada kansu duk da bambance- bambancensu; ga kuma samar da abubuwan more rayuwa a kauyuka, farfado da lamarin kula da lafiyar al’umma, taimaka wa manoma da matasa yadda za su tsaya da kafafunsu; tafiyar da gwamnati ta tausaya wa al’umma, yin biyayya da dokoki, da tunanin yadda gaba za ta yi kyau; shi ya sa aka zabi Sanata Uba Sani a matsayin Gwarzon Gwamnan shekarar 2025.

Sanata Uba Sani: Mai Hada Kan Al’ummar Da Suka Rarrabu

Gwarzon Dan Majalisa Na Shekarar 2025

8. Saboda yadda ya shahara wajen yin doka, wakilci, nuna damuwa da sai abu ya kasance; yadda yake da hazaka, sa ido kan ci gaban inda yake wakilta, da kokarin samar da zaman lafiya, tsarin da ya sa aka samu cimma buri a gyaran tsarin mulki, hadin kan kasa;. Honorabul Benjamin Okezie Kalu, PhD, CFR don haka shi ne dan majalisar shekarar 2025.

Benjamin Okezie Kalu: Wakili A Majalisa Saboda Hadin Kan Kasa, Zaman Lafiya, Da Ci Gaba

Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025

9. Bisa la’akari da yadda ya tafiyar da sha’anin kawo gyara a lamarin tara haraji, abin da aka aiwatar ta yadda ya dace a yi da gaskiya domin habbaka hanyoyin samun kudaden shiga ba ta hanyar man fetur ba, amma ta hanyar bullo da wasu dabaru ta kafar sadarwa ta zamani; da yake an dauki hukumomin gwamnati da su ma abokan tafiya ne domin samun ci gaba, ba tare da an sa wani abu na matsi ba; Dakta Zacch Adedeji a yanzu shi ne gwarzon ma’aikakaci na shekarar 2025.

Dakta Zacch Adedeji: Wanda Ya Kara Daukaka Darajar Haraji A Nijeriya

Gwarzon Dan Kasuwa Na 2025

10. Saboda hangen nesansa wajen kawo gyara a lamarin bunkasa samar da takin zamani a Nijeriya da kuma harkar kasuwancin amfanin gona; don tallafa wa miliyoyin manoma hanyar amfani da abubuwan gida. Da kuma kokarinsa na samar da wata hanyar taimakawa masu karamin karfi yadda za su cimma burinsu na maida aikin gona a matsayin wata hanya da za ta taimaka wa al’umma; don haka Thomas Etuh shi ne gwarzon Dan kasuwa na shekarar 2025.

Thomas Etuh: Gwarzo Wajen Samar Da Hanyoyin Dogaro Da Kai Ga Matasa

Gwarzon Shugaban Kamfani Na Shekarar 2025

11. Domin jagorantar bangaren hakar mai da iskar gas na tekun Nijeriya da ya yi nasarar samar da ganga miliyan 1.8 na man fetur a kowace rana; da kuma jagorantar hukumar NUPRC ta zarce burinta na samun kudaden shiga da kashi 84.2 cikin dari, Injiniya Gbenga Komolafe shi ne Gwarzon Shugaban Kamfani na Shekara ta 2025.

Gbenga Olu Komolafe: Jagorantar Tsarin Samar Da Makamashi A Nijeriya

Gwarzon Ma’aikacin Banki Na Shekarar 2025

12. Domin jagorantar harkar kudi ta hanyar kirkire-kirkire tare da karfafa samar da kanana da matsakaitan sana’o’i (MSME) 700,000 da karfafa tubalin tattalin arzikin Nijeriya da kuma sake fasalta banki; an zabi Dakta Tony Okpanachi a matsayin Gwarzon Ma’aikacin Banki Na Shekarar 2025.

Dr Tony Okpanachi: Gina Makomar Nijeriya Ta Hanyar Tallafa Wa Kananan Kamfanoni

Wanda Da Ya Fi Tasiri A Kafofin Sada Zumunta Na Shekarar 2025

13. Domin sauya rikici zuwa hadin kai, da tashin hankali zuwa ci gaba mai ma’ana da kirkirar ayyukan yi, samar da zaman lafiya da sabunta zamantakewa, al’adu da tattalin arzikin Neja Delta da zuba jari a ilimi, kiwon lafiya, muhalli da karfafa ci gaba, an zabi Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo) a matsayin mafi tasiri a Kafofin Sada Zumunta na 2025.

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

Gwarzuwar Hukumar Gwamnati Ta Shekarar 2025

14. Domin fadada iyakokin aiwatar da doka a Nijeriya tare da dawo da fiye da naira biliyan 10 ga masu amfani da kayayyaki tare da kalubalantar rashin adalci na kamfanoni da kafa sabbin ka’idoji kula da kasuwanci ta kafafen sadarwar zamani da tabbatar da adalci da shugabanci na na gari — Hukumar Kare ‘Yancin Masu Amfani da Kayayyaki ta Kasa (FCCPC), ita ce Gwarzuwar Hukumar Gwamnati ta Shekarar 2025.

Hukumar Kare ‘Yancin Masu Amfani Da Kaya (Fccpc): Tabbatar Da Adalci A Kasuwa

SkalesShi Ne Gwarzon Mawakin Shekarar 2025

15. Sakamakon tasirin da ya dade yana yi a fannin waka a Nijeriya da kasashen waje. Shahararriyar wakarsa “Shake Body”, wacce ta kai ga samun miliyoyin masu sauraro a Spotify da kuma kwarewarsa a fannin fasahar hada al’umma daban-daban. SKALES ne Gwarzon Mawakin Shekarar 2025.

Kanyenyachukwu Tagbo Okeke Shi Ne Gwarzon Mai Zane Na Shekarar 2025

16. Saboda sanya Nijeriya a taswira ta duniya tare da Guinness World Record (GWR) na Mafi Girman Zanen Canbas da mutum daya ya yi a wannan shekara, da kuma wayar da kan jama’a kan cutar autism a Nijerriya, tare da amfani da fasaha wajen karfafa hadin kai da ilimi ga mutane masu kwarewa daban-daban, Kanyenyachukwu (wanda aka fi sani da Kanye) Tagbo-Okeke shi ne Gwarzon Mai Zane na Shekara 2025.

Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025

17. Saboda jagorantar Super Falcons zuwa nasarar lashe kofin WAFCON karo na 10, wanda ya kara musu tasiri; da nuna kwarewa a dabaru da shugabanci da dawo da aminci a kwallon kafar Nijeriya da kuma karfafa sabon karni na masu horar da kwallo a Afirka, Justine Madugu shi ne gwarzon mai koyar da wasanni na Shekarar 2025.

Justine Madugu: Mai Dabaru Dawo Da Darajar Kwallon Kafa A Nijeriya

Dabid Adeyemi Shi Ne Gwarzon Matashi Na Shekara 2025

18. Dangane da habaka kirkira, tausayi da kwarewa ta hanyar kirkirar manhajar AI wacce ke sauya yadda dalibai masu nakasar gani ke samun ilimi a Nijeriya da wajenta, Dabid Adeyemi shi ne Gwarzon Matashi na Shekarar 2025.

Gwarzon Ma’aikacin Lafiya Na Shekarar 2025

19. Domin ganin yadda ya sauya akalar samar da kiwon lafiya cikin tausayi da soyayya ga mabukata tare da yi wa mutane fiye 2,600 tiyata kyauta a sassan kasar nan. Dr Seidu Adebayo Bello shi ne Gwarzon Ma’aikacin Kiwon Lafiya na shekarar 2025.

Dr Seidu Adebayo Bello: Ya Dawo Da Fata Ga Al’umma

Misis Mabel Ijeoma Duaka Shi Ne Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025

20. Duk da ayyukan ta’addanci na Boko Haram, yayin da al’umma musamman baki ke gudu daga yankuna da dama na Jihar Borno, ta gwammace ta zauna a karamar hukumar Mafa domin ci gaba da bayar da kulawa ga wadanda suka jikkata na tsawon shekara 21. Mrs Mabel Ijeoma Duaka ce Gwarzuwar Ma’akaciyar jinya ta shekarar 2025

Bankin Probidus Ne Gwarzon Banki Na Shekarar 2025

21. Saboda kasancewa kan gaba wajen zamanantar da harkokin Banki a Nijeriya da kuma karfafa wa manya da kananan masa’na’antu tare da zama a kan gaba wajen daukaka darajar aikin Banki a Nijeriya, Bankin Probidus ne Gwarzon bankinmu na shekarar 2025.

Gwarzuwar Matashiya ‘Yar Makaranta Ta Shekarar 2025

22. Domin nasarar da ta samu wajen sanya sunan Nijeriya a fagen ilimi a duniya da jajircewa, hazaka da bayar da shawarwari don zaburar da sabbin dalibai don rungumar harshe Turanci da tabbatar da nasara na iya tasowa daga kowane bangare. An bai wa Nafisa Abdullahi Aminu lambar yabo ta Gwarzuwar Matashiyar 2025.

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Daukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

Hukumar NASENI Ne Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025

23. Domin yadda ta jagoranci ci gaban masana’antu, samar da makamashi, da fasahohin da suka dace da yanayin da ke rage fitar da iskar carbon mai guba da inganta hanyoyin samar da wutar lantarki mai tsabta; karfafa masu kirkire-kirkire na cikin gida, samar da dabarun tattalin arzikin mai dorewa, da habaka dogaro da kai a Nijeriya ta hanyar bincike da kula da muhalli, Hukumar NASENI ce Gwarzuwar Hukumar da ta fi tasiri wajen kare muhalli a shekarar 2025.

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kudade Na Shekarar 2025

24. Don kawo sauyi a harkokin kudade ta hanyar fasahar zamani da suka hada da kirkira da gaskiya wajen karfafa miliyoyin ‘yan Nijeriya, kanana da matsakaitan kamfanoni (MSME) ta hanyar amfani da wayar hannu, don kawo karshen matsalolin kudade ta hanyar fasahar zamani, OPay Nigeria ya amsa sunansa na zama gwarzon kamfanin fasahar harkokin kudade na shekarar 2025.

OPay Nigeria: Tabbatar Da ‘Yancin Hada-hadar Kudi

Kamfanin GEIL: Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025

25. Domin jagorantar bunkasawa da gudanar da tashar fitar mai na farko a Nijeriya fiye da shekaru 50, Kamfanin GEIL shi ne Gwarzon Shekarar 2025

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025

26. Domin habaka samar da ruwan sha mai inganci da arha, dandano da wayar da kan ‘yan kasa kan amfani da tsaftataccen ruwa, kamfanin Nestlé Pure Life Nigeria Plc shi ne gwarzon samar da kaya a shekarar 2025.

Kamfanin Nestlé Pure Life: Tsarinsa Da Manufa

Kamfanin Trade Modernisation Project: Gwarzon Kamfani Na Shekarar 2025

27. Domin sauya tsarin kasuwancin Nijeriya ta hanyar fasahar zamani da inganci, sarrafa ayyuka, kara habaka samun kudaden shiga da saukaka gudanar da kasuwanci, bunkasa hadin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu, samar da ayyukan yi da karfafa gasa, Kamfanin Trade Modernisation Project (TMP) shi ne gwarzon Kamfanin shekarar 2025.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari October 31, 2025 Manyan Labarai An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano October 31, 2025 Labarai Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai  October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure