Aminiya:
2025-05-01@04:45:00 GMT

Yadda Kano ke samar da madarar Naira biliyan 2.2

Published: 8th, February 2025 GMT

Madara muhimmin abinci ne da ake bukata domin samun sinadarai masu ginawa da ƙara ƙarfi da lafiyar jiki.

Bincike ya nuna cewa mutane biliyan shida ne ke shan madara a duniya, wanda ya sa shan madarar saniya da kiwon dabbobi ya zama wani vangare na rayuwar ɗan adam.

Dubban mata Fulani suna samun kuɗaɗen shiga ta hanyar sayar da madara ga ɗaiɗaikun mutane ko jama’a ko ’yan kasuwa, waɗanda suke sha ko sarrafa shi domin amfanin kasuwanci.

Lura da muhimmancin madara ga rayuwar ɗan Adam da kuma ƙoƙarin rage haɗarin da ke tattare da shan ta, Hukumar Haɓaka Noma da Kiwon Dabbobi ta Jihar Kano (KSADP) ta zuba jarin Dala miliyan 8.03 don gina cibiyoyi 100 na tattara madara a jihar, da nufin tallafa wa makiyaya domin su wadatar da buƙatun masana’antar madara da sauran masu buqatar ta.

An tallafa wa Ƙungiyar Masu Sayar da Madarar Saniya ta Kasuwar Ƙofar Wambai da ɗakin ajiye kayan sanyi domin tabbatar da tsafta da kuma ingancin madara.

An kashe ɗan banga da yin garkuwa da ’yan mata 6 a Neja An dakatar da dagaci kan zargin saran maraya da adda

Shugaban ƙungiyarsu, Alhaji Muhammad Alaramma, ya ce harkar kiwon dabbobi na bunqasa sosai a Jihar Kano sakamakon matakin da gwamnatin jihar ta ɗauka ta hanyar hukumar KSADP, wadda ta ba wa ƙungiyar tallafin wurin ajiye kayan sanyi.

Lita dubu hamsin a kullum

“Kullum ana sayar da aqalla lita 50,000 na madara, amma wani lokaci ba ya kaiwa haka, saboda qarancin madara a Kano a halin yanzu. Mutane sukan kawo shi daga Jos da Bauchi da Jama’are da sauran wurare.

“Wurin ajiyar kayan sanyi da aka ba mu yana da matuqar amfani, amma ƙalubalen shi ne ba ya amfani da lantarki mai amfani da hasken rana. Amma mun yi yarjejeniya da wani wanda ya karɓi hayar wani vangare na wajen, shi kuma a madadin haka yana ba mu wutar lantarki, daga injin ɗinsa.

“Naira 200 muke karva a kan kowane bokitin madara da aka kawo ajiya daga hannun ’ya’yan qungiyarmu, waɗanda sun kusa mutum 20,000,” in ji shugaban ga wakilinmu.

Barazanar ƙwayar cuta

Madarar da aka sarrafa na iya harbuwa da ƙwayar cuta idan ba a kiyaye ta ba, wanda hakan na iya shafar lafiyar ɗan Adam. Masana sun bayyana cewa kashi 70 cikin 100 na cututtukan da ke damun xan adam suna da alaƙa da dabbobi. Don haka shan madara mara tsafta na iya zama babban haxari ga lafiyar ɗan Adam.

Shirin Haɓaka Noma da Kiwon Dabbobi na Jihar Kano, tare da tallafin Bankin Ci-gaban Islama (IsDB) da Asusun Inganta Rayuwa (LLF), na gina cibiyoyi 100 na tattara madara a Kano don inganta samuwar madara domin kasuwanci da ɗaga darajarta, da kuma magance matsalar qarancinta da rashin ingancinta a harkar kasunwancin.

Wani ƙwararre kan kiwon dabbobi a KSADP, Dakta Garba Saleh, ya bayyana cewa ana gina cibiyoyin madarar ne domin tattara ta daga makiyaya domin a ci gaba da raba wa masu sarrafawa.

“Manufar ita ce tabbatar da tsafta da ingancin madara, ta yadda duk sinadaran da suka dace ba za a lalata su ba. Idan babu cibiyar tarawa za a iya rasa mahimman sinadaran da ke cikin madara cikin sauƙi.

“A ƙarƙashin shirin, za a kafa cibiyoyin tattara madara (MCC) guda 100 inda a halin yanzu an kammala 40 daga ciki.”

Yawa da darajar madarar

Ƙwararrun a fannin kiwon dabbobi ya bayyana cewa ana sa ran kowace cibiyar za ta ajiye aƙalla lita 28,000 na madara a mako, kimanin lita miliyan 1.46 a kowace shekara. Hakan nan nufin yawan dararar cibiyoyin guda 100 za su adana a shekara ya kai lita miliyan 146.

Ana kuma sa ran makiyaya 25 za su riƙa ba wa kowane MCC madara, ta yadda kowane MCC zai riƙa samar da Naira 4,622,872 a duk mako.

A wata guda zai samar da kimanin Naira miliyan 18.5, wato Naira miliyan 221 a duk wata. Hakan na nufin za a samu jimillar Naira biliyan 2.2 (Dala miliyan 1.4) daga MCC 100 ɗin a shekara.

Yadda cibiyoyin suke

Kowace cibiya tana amfani da wutar lantarki mai amfani hasken rana kuma tankin sanyaya abubuwa wanda aka qera da qarfe mara yin tsantsa; da kuma injin tata da famfo da na’urar xumama ruwa da kayan gwajin madara da na tsaftar muhalli da mazuban tattara madara da rijiyoyin burtsatse masu tankin sama.

Zuwa yanzu, an gina cibiyoyi biyar a Doguwa, huɗu a Albasu, huɗu a Danbatta, sannan uku-uku a Dansoshiya a Ƙaramar Hukumar Kiru da Garko da Garun Malam da Tofa da Kura da Dawakin Tofa.

Makiyaya na murna

Wani Bafulatani makiyayi a ƙauyen Ɗansoshiya, Muhammad Major, ya ce duk da cewa an an kammala cibiyar tara madarar yankinsu, amma dai ba ta fara aiki ba, amma duk da haka makiyaya suna farin ciki da kafa cibiyar.

Muhammad Major ɗan shekara 52 ya ce, “An kammala cibiyar Ɗansoshiya amma ba ta fara aiki ba, don haka Kano muke kai madara mu sayar. Amma idan ya fara aiki, nan zan riƙa kaiwa a ba ni kuɗina ba sai na kashe kuɗin mota zuwa Kano ba, ka ga na rage kashe kuɗi.”

Manyan kanfanoni irin su L&Z sukan yi amfani da cibiyoyin da KSADP ta kafa baya ga nasu na ƙashin kansu, ci-gaban kasuwancinsu.

Barazanar manyan kamfanoni

Wasu da ke harkar kuma sukan yi amfani da madarar gari ko waken suya, domin haɗawa da madarar shanun da suka samu daga masu kawo musu, wadda ta yi karancin sosai.

Wata Bafulatana da ke kawo nono Kano daga Bunkure, Hauwa’u Abubakar, ta ce ba a kafa irin wannan cibiya a yankinsu ba. Hauwa’u takan kashe kuɗin mota N1,000 a kullum zuwa Kano inda take sayar da bokiti uku zuwa biyar na nono kowanne a kan kimanin N6,5000, a duk tafiya.

Hauwa ta ce, “Kullum nan (Kano Line) nake kawo bokiti uku zuwa biyar na nono, inda muke sayar da duk bokiti a kan N6,500. Wasu a nan suke saya su kai Kasuwar Ƙofar Wambai su sake sayarwa, amma na fi so in tsaya a nan a saboda in rage kashe kuxin abin hawa.”

Shi ko Abdulmuɗɗalibi Sani, wanda ke sana’ar fura da nono, yakan sayi nono ne a wurin matan Fulani a cibiyar da ke Kano Line. Ya ce ya sayi bokiti shida saboda ya ya fi arha idan aka kwatanta da na Kofar Wambai, inda dillalai kan yi amfani da damar su ƙara farashi.

Ya ce ƙananan masu sayen nono irinsa na fama da manyan kamfanoni irin su L&Z da ke harkar, waxanda suke da nasu cibiyoyin tattara madara inda suke saya kai-tsaye daga hannun makiyaya.

Abdulmuɗɗalibi ya ce “Manyan mutane da ke saya kai-tsaye daga wurin matan Fulani su ke haddasa ƙarancin madara da tsadarsa, amma kuɗinsa bai kai haka ba.”

Wai mai sayar da madara, Awwal Sa’id wanda yakan sayi bokiti biyar zuwa shida a Kano Line ya ce, abin da ya jawo shi shi ne cinkoson da ke Ƙofar Wambai da kuma yadda dillalai ke sanya farashi.

Yadda za a bunƙasa harkar

Wani qwararre a fannin kiwon dabbobi a Hukumar KSADP, Dakta Garba Saleh, ya yi imanin cewa kasuwancin madara zai samu ci-gaba sosai a nan gaba.

Ya bayyana cewa ko da yake a halin yanzu Nijeriya ba ta samar da madarar da za ta wadatar da buqatar cikin gida, za a kai lokacin da qasar za ta riƙa fitar da ita zuwa ƙetare idan aka haɓaka tare da tallafa wa harkar.

Ya ce ƙasashen Kenya da Uganda da Rwanda sun bunƙasa fannin madararsu ne ta hanyar taimako da tallafa wa ƙananan kamfanoni domin fitar da ita zuwa qasashen qetare.

Qalubalen harkar

Sai dai kuma shanu ’yan qasa na daga cikin ƙalubalen. Dakta Saleh ya bayyana cewa shanu ’yan qasa ba sa samar da madara mai yawa, domin abin da suke samarwar a yini guda bai fi lita uku zuwa biyar ba, idan aka kwatanta da shanun qasashen waje da ke ba da lita 50 a kullum.

Sannan kuma ciyawa ’yar ƙasa ba ta da sinadaran gina jiki sosai, sannan yin kiwo ba tare da gandun kiwo ba, babu riba.

Ya ce domin magance wannan matsala Hukumar KSADP tana aiki a wani fili mai fafin hekta 3,000 inda za a noma nau’ika daban-daban na ciyayi da aka ƙara wa inganci, irin su nau’in Nafia da Stylo da kuma Gamba.

Hukumar KSADP na kuma aikin yin barbarar shanu ’yan qasa da na waje domin ganin sun samu siffofi da nagartar ’yan ƙasar waje.

Kafa Ma’aikatar Kiwon Dabbobi zai iya kawo sauyi ta hanyar samar da ingantaccen abincin dabbobi wanda zai inganta samar da madara mai nagarta da yawan gaske wanda hakan zai kawo riba mai tsoka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: madara ya bayyana cewa samar da madara Ya bayyana cewa tattara madara Hukumar KSADP

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja

Rayukan al’umma gami da dukiya musamman na ababen hawa na ci gaba da salwanta a Mahadar hanya ta yankin Tipper-garage da ke Dutse-Baupma, da ke kan titin da ya tashi daga garin Dutsen-Alhaji ya nufi garin Bwari, a yankin Birnin Tarayya Abuja.

Titin da ke mastayin tagwaye ya haɗa yankin da garin Jere da ke Jihar Kaduna.

Hanyar na ci gaba da ganin ƙaruwar kwararan motoci a sakamakon ingancinta da kuma karancin matsalar tsaro, idan a ka kamanta ta da babban titi Abuja zuwa Kaduna.

Rawar da Arewa za ta taka a Zaɓen 2027 An ɗaure ’yar shekara 80 a kurkuku saboda dukan jikarta da silifas

Adadin motoci da ke bin titin ya kara dagawa a bayabayan nan a dalilin mummunan cunkushewar hanya da ake fuskanta a garin Zuba Abuja da kuma Madalla da ke Jihar Neja, a sakamakon rufe hannu guda na hanyar biyo bayan fara aikinsa da wani sabon kamfani ke yi, bayan karbe aikin daga kamfanin Bega.

Baya ga motoci na matafiya da ke yawan ratsawa ta hanyar, akwai kuma motocin tifa da ke daukar duwatsu daga kamafanonin fasa duwatsu biyu da ke kusa da mahadar hanyan suna kai wa yankuna daban-daban na Abuja dama kewaye.

Aminiya ta ba da labarin cewa hatsarin mota na baya bayan nan da a ka fuskanta a hanyar su ne wanda ya auku a ranar Asabar 5 ga wannan watan na Afrilu, 2025, inda a ka rasa rayukan mutum biyar, bayan wata babbar mota tirela da ta fito ta kusurwan Bwari ta fuskanci matsalar tsinkewar birki a yayin da ta ke gangarowa daga hayin madatsar ruwa na Usuma dam da ke kan titin.

Tirelar ta taka kekunan adaidaita sahu guda biyar da ke daukar fasija a gefen hanayar, baya ga wani adadi na baburan acaba.

Kwana biyu bayan aukuwar hatsarin, an sake fuskantan wani a ranar Litinin da ta biyo baya inda wata babbar mota irin ta daukar bulo da ke dauke da albasa daga wata jiha ta Arewa ta rasa birki a yayin saukowa daga gangarar hanyar.

Ta buge kekunan kafin ta kife a kusa da wani magudanan ruwa da ke jikin hanyar.

An bada labarin rasa mutum biyu a yayin hatsarin, baya ga wasu da su ka tsira da raunuka.

Asarar rayuka da ta dukiya da muka yi — Masu tukin adaidaita sahu

Malam Fahad Musa na cikin shugabannin kungiyar ’yan yuniyon na masu sana’ar tukin Keken Adaidaita sahu da ke aiki a wurin.

Ya ce hatsarin farko ya faru ne da misalign karfe 7 na dare inda ya ce sun rasa mambobinsu uku, sai kuma dan acaba guda, a yayin da mutum na biyar din kuwa ya rasa ransa ne a dalilin harbinsa da bindiga da ake zargin wasu da suka taho cikin ayarin motoci suka yi, kamar yadda majiyoyi daban-daban suka shaidawa Aminiya.

Shugaban na ’yan yuniyon ya shaida wa wakilinmu a yayin ziyara a wajen cewa an kuma rasa kekune biyar a yayin hatsarin bayan motar ta bi ta kansu.

Ya ce faduwar motar ta farko ta yi sanadiyyar rufe hannu guda sannan ba a kai ga cire ta ba sai bayan hatsari na biyu a ranar Litinin.

Ya ce, a lokacin da ake kokarin zakulu mutane da suka mutu da kuma wadanda suka yi raunukan daga karkashin ababan hawan a ranar Asabar, an rufe daukacin tagwayen titin biyu da lamarin ya kai ga jawo takaddama bayan ayarin jami’an tsaro sun bulla ta wajen.

Wani da ya shaidi lamarin, ya shaida wa Aminiya cewa, a lokacin da ayarin motocin suka bullo, wani babba a cikin tawagar ya fito daga cikin mota tare da neman da a bude masu daya hanyar, amma sai ’yan asalin al’ummar yankin suka ki amincewa da bukatar hakan.

Ya kara da cewa, matasan sun bi motocin ayarin da jifa bayan sun kutsa ta daya hanyar da nufin wucewa, kuma a nan ne sai wasu daga cikin jami’an tsaron suka yi harbi cikin iska, a yayin da wani kuma ya harbi daya daga cikin matasa ’yan asalin yankin mai suna Timothy John, da ya mutu nan take.

Bayan nan, ayarin sun wuce da motocinsu cikin hanzari, kamar yadda aka bayyana wa Aminiya.

A yayin zantawarsa da Aminiya shugaban n ’yan yuniyon na masu sana’ar tukin adaidaita sahu ya ce, daya daga cikin direbobinsu mai suna Yusuf Auwal na cikin wadanda harsashin bindiga ya bi ta jikinsa.

Ya ce, bayan nan an garzaya da shi zuwa garinsu inda yake cigaba da jinya a yanzu.

Babban Kwamandan Hukumar Kare Hadurra na FRSC mai kula da yankin Dutsen-Alhaji, Mista Luka Wuna, ya tabbatar da faruwan haduran biyun, da kuma rasa rayukan, a yayin zantawarsa da wakilinmu a kan lamari.

Akwai bukatar ilimantar da direbobin Tifa

Binciken Aminiya ya bayyanan cewa, matsalar da tifofi ke samu ta shanyewar burki a yayin da suka ɗauko kaya kuma suka sukwano gangarar da daga ita sai marabar titin ita ce a mafi yawan lokaci ke haddasa munanan hadurra a wannan mahada.

Da yawan direbobin tifa matasa ne da basu san dokokin tuki ba sannan kuma suna tukin da ganganci tamkar suna tuka kananan motoci.

Don haka mafi yawa ba sa kula da yadda suke shawo wannan gangara ta la’akari da cewa, burkin tifa iska ce.

Wani masanin harkokin sufuri da ba ya son a ambaci sunansa ya ba da shaara cewa, ya kamata hukumomin da abin ya shafa su rinka shirya wa direbobin musamman na Tifa bita kan ka’idojin tuki da alamomin hanaya da kuma hatsarin da ke tattare da burkin mota mai dauke da iska.

Abinda ke jawo hatsari a wajen

Malam Anas Mu’azu na cikin ma’aikatan tattara haraji na Karamar Hukumar Bwari da ke ba da tikiti a wajen.

Ya ce, yawancin direbobi da ke fuskantar hatsarin baki ne da ke bi ta gangaren hanyar ba tare da cikakken masaniya a kan yadda wajen yake ba.

Ya ce, ”wutar ba da umarnin wucewa a wajen da ke da kusurwa 4 na bukatar tsayawar mota na wani lokaci a duk ta inda ta fito saboda dogon layi da motoci ke yi, sannan indan wutar ta haska don wucewa, adadi kadan ne na motoci ke iya wucewa kafin ta sake bukatar tsayar da mota,” in ji shi.

Malam Anas ya kara da cewa yawancin bakin direbobi da ke bin hanyar ba su da masaniya a kan tsarin wutar da kuma yanayin hanyar kasancewar babu allunan alamomi na hanya da ke fadakarwa a kan titin.

Ya ce, haka kuma a baya an cire kunyar kan titi da ke sa motoci rage gudun mota. ”A baya akwai kunyar titi na rage gudun da adadinsu ya kai kamar guda biyar, amma sai a ka cire su a lokaci guda ta hanyan kankare su daga kan hanyar,” in ji shi.

Ya ce, ko da Ministan Birnin Abuja Mista Nyesom Wike ya ba da aikin sake gina hanyar a bayabayan nan, ba a maida kunyar titin ba, har zuwa lokacin da haduran baya-bayan nan su ka auku..

Yadda za a magance matsala —Masu Tifa

Haka kuma Aminiya ta zanta da daya daga shugabannin masu motocin tifa da kuma harkar sayar da duwatsu daga kamfanoni biyu na fasa dutsi da ke yankin mai suna Kwamred Ose Idasho inda ya ba da shawarwaari kan yadda ya ke ganin za a magance yawaitar haduran, da ya ce sun bayar a yayin wani zama na musamman da Jami’an Hukumar Magance Hadurra ta FRSC a yankin.

Ya ce, “abu na farko shi ne bukatar a sa alamomin hanya tun daga kamar kilo mita uku kafin mahadar hanyar da zai rika sanar da direba hatsarin wajen tare da bukatar da ya yi takatsantsan.

“Sai kuma a sa abubuwa da ke sa rage gudun mota na kunyar hanya samfurin roba ba na siminta ba, da zai rika yin kara idan direba ya yi yunkurin yin gudu sosai. Hakan zai kara wa direba karsashi ko da ya fara yin gyangyadi.

“Mun kuma bukaci jami’an na FRSC da nemi dauki daga Hukumar Kula da Gine-gine ta Abuja kan su kawar da wuraren da ke sa mutane na tsayawa ta wurin, tare da mayar da shi sarari, sai kuma samar da wurearen yin lodi da kuma hana yin lodi a gefen titin.

“Haka kuma akwai bukatar a gyara wasu daga cikin fitilun ba da hannu da suka daina yin aiki, kamar wanda ya shiga ta bangaren Bamuko ta inda motocin tifa ke shiga da kuma yawan fita.

Sai kuma uwa-uba a gina gadar sama a wajen da zai rage girman gangarowar motoci da ke fitowa ta kusurwar Bwari ko DutsenAlhaji inda motocin za su bi ta saman gada,” in ji jagoran masu motocin tifa.

Ya kamata a gina gadar sama

Shi ma a zantawarsa da Aminiya, Sakataren Hakimin yankin na Dutse-Baupma mai suna Simon Luka da ya yi bayani a madadin hakiminsu, ya ce, hatsarin motoci a wajen ya jima yana jawo masu fargaba da kuma asarar rayuka da dukiya.

Ya buƙaci Ministan Birnin Tarayya Mista Nyesom Wike da ya taimaka wajen yin aikin gadar sama a wajen don magance matsalar.

Ya ce, tarihin farawar matsalar ba za ta gaza shekara 20 bayan an yi aikin hanyar.

Ya ce, matashin da aka kashe bayan jami’an tsaro sun buɗe wuta a wajen mai suna Timothy John, bai wuce shekara 20 ba kuma lamarin ya faru ne kasa da mako guda bayan mai gidansa ya yaye shi daga aikin walda da ya ke yi, inda yake shirin buɗe na kansa.

Ya kara da cewa, “sai dai har zuwa lokacin ziyarar nan babu wata ta’aziyya ko ta jaje da muka samu daga jamiu’an tsaro ko kuma hukuma, kan mutuwar matashin.”

Aminiya ta tuntubi Babbar Jami’ar Hulda da Jama’a a Sakatariyar da ke Kula da Sufuri a yankin Birnin Tarayya Abuja mai suna Misis Lecita Wogu, inda ta buƙaci lokaci don yin tsokaci a kan lamarin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwastam Ta Kama Jirage Marasa Matuka Da Sauran Kayayyaki Da Darajarsu Ta Haura Naira Biliyan 921 A Legas
  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • Makiyayi Ya Kashe Abokai 2 A Nasarawa Kan Rikicin Kiwo
  • Kotu Ta Kori Ƙarar Neman Diyyar N1bn A Kan Buhari Da Emefiele Kan Sauya Fasalin Naira
  • HKI Tana Amfani Yunwa A Matsayin Makamin Yaki  A Kan Falasdinawa A Gaza
  • Sin Za Ta Aiwatar Da Matakan Daidaita Samar Da Guraben Ayyukan Yi Da Raya Tattalin Arziki
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026
  • Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi
  • Ma’aikata 240 na karɓar albashi biyu, wasu 217 na amfani da lambar BVN ɗaya a Kano