Aminiya:
2025-09-18@00:00:54 GMT

Amurka ta dakatar da bai wa Afirka ta Kudu tallafi

Published: 8th, February 2025 GMT

Gwamnatin Amurka ta sanar da janye tallafin da take bai wa Afirka ta Kudu yayin da alaƙa tsakanin ƙasashen biyu ta lalace a dalilin dokar karɓe gonakin fararen fata da Shugaba Cyril Ramaphosa ya amince da ita.

Shugaba Donald Trump ya ce Amurka za ta katse duk wani tallafin da take ba wa Afirka ta Kudu ciki har da na kuɗi a wani mataki na nuna adawa da dokar kwace filayen noma da Shugaba Cyril Ramaphosa na kasar ya rattabawa hannu.

Yadda rikicin shugabanci ya janyo rufe babban masallacin gari Yadda Kano ke samar da madarar Naira biliyan 2.2

Shugaba Trump ya ce Amurka ba za ta taimaka wa gwamnatin Pretoria ba, duba da yadda take ci gaba da take haƙƙin ɗan Adam, da kuma yi wa siyasar Amurka ta ƙetare karan tsaye, inda ya soki zargin Isra’ila da aikata laififukan yaƙin da Afirka ta Kudun ta yi a baya, da ma hulɗarta da Iran a wani ƙudirin da ya sakawa hannu a ranar Juma’a.

Sai dai tun a gabanin matakin na shugaban Trump ya soma aiki, a wani jawabinsa, Shugaba Cyril Ramaphosa na Afirka ta Kudun ya ce kasarsa ba za ta kawar da ido ga duk wata barazana ba.

Tun farkon wannan wata na Fabrairu ne Donald Trump ya ce zai yanke duk wasu kuɗaɗe da Amurka ke bai wa Afirka ta Kudu har sai an kammala cikakken bincike kan matakin gwamnatin ƙasar na ƙwace filaye mallakar fararen fata ba bisa ƙa’ida ba.

Barazanar na zuwa ne yayin da a ƙarshen watan Janairun da ya gabata Shugaba Ramaphosa ya ƙaddamar da dokar da ta bai wa gwamnati damar ƙwace wasu filaye galibi mallakin fararen fata ba tare da biyan diyya ba a wani mataki na samar da daidaito da kuma adalci ga ’yan kasar.

Gwamnatin Afirka ta Kudu ta bayyana matakin a matsayin wani yunƙuri na gyaran kura-kurai na rashin daidaito da ƙasar ta gada daga Turawan mulkin mallakar na Birtaniya.

Sai dai wannan mataki ya gamu da suka daga masu ra’ayin mazan jiya ciki har da attajirin nan Elon Musk ɗan asalin Afrika ta Kudu wanda ke da kusanci da shugaba Donald Trump.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: wa Afirka ta Kudu

এছাড়াও পড়ুন:

DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu

Hukumar Tsaron Farin Kaya a Nijeriya DSS, ta gurfanar da fitaccen ɗan gwagwarmayar nan, Omoyele Sowore a kotu.

A ƙunshin ƙarar da DSS ta gabatar a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta haɗa da shafukan sada zumunta na X da kuma Facebook, inda take zarginsu da ba da ƙofar aibata Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Bida Poly ta sa sojoji kula da jarrabawar ɗalibai Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku

Darekan shigar da ƙara na Ma’aikatar Shari’a ta Tarayya, M.B Abubakar da wasu lauyoyi huɗu —M.E. Ernest da U.B. Bulla da C.S. Eze da kuma E.G. Orubor, ne suka shigar da ƙarar a madadin Gwamnatin Tarayya da kuma hukumar ta DSS.

DSS wadda ta kafa hujja da sashe na 24 da ke cikin kundin dokokin yanar gizo, ta ce Sowore ya yi amfani da shafukansa na dandalan sada zumunta na X da Facebook wajen wallafa wani saƙo da ke cin mutuncin Shugaba Tinubu.

Tun dai a farkon watan nan ne DSS ta buƙaci goge wani saƙo da ɗan gwagwarmayar ya wallafa wanda ta riƙa a matsayin bayanan ƙarya, cin zarafi ta yanar gizo da kalaman haddasa ƙiyayya, waɗanda kuma ta ce na iya haddasa rikici su kuma ɓata sunan Najeriya a ƙasashen waje.

Sai dai har zuwa ranar Litinin, 15 ga watan Satumba, babu wani mataki da aka ɗauka na goge saƙon da DSS ɗin ta buƙata.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
  • NECO ta saki sakamakon jarabawar 2025
  • An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin
  • Fizishkiyan:  Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI
  • Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila