Amurka ta dakatar da bai wa Afirka ta Kudu tallafi
Published: 8th, February 2025 GMT
Gwamnatin Amurka ta sanar da janye tallafin da take bai wa Afirka ta Kudu yayin da alaƙa tsakanin ƙasashen biyu ta lalace a dalilin dokar karɓe gonakin fararen fata da Shugaba Cyril Ramaphosa ya amince da ita.
Shugaba Donald Trump ya ce Amurka za ta katse duk wani tallafin da take ba wa Afirka ta Kudu ciki har da na kuɗi a wani mataki na nuna adawa da dokar kwace filayen noma da Shugaba Cyril Ramaphosa na kasar ya rattabawa hannu.
Shugaba Trump ya ce Amurka ba za ta taimaka wa gwamnatin Pretoria ba, duba da yadda take ci gaba da take haƙƙin ɗan Adam, da kuma yi wa siyasar Amurka ta ƙetare karan tsaye, inda ya soki zargin Isra’ila da aikata laififukan yaƙin da Afirka ta Kudun ta yi a baya, da ma hulɗarta da Iran a wani ƙudirin da ya sakawa hannu a ranar Juma’a.
Sai dai tun a gabanin matakin na shugaban Trump ya soma aiki, a wani jawabinsa, Shugaba Cyril Ramaphosa na Afirka ta Kudun ya ce kasarsa ba za ta kawar da ido ga duk wata barazana ba.
Tun farkon wannan wata na Fabrairu ne Donald Trump ya ce zai yanke duk wasu kuɗaɗe da Amurka ke bai wa Afirka ta Kudu har sai an kammala cikakken bincike kan matakin gwamnatin ƙasar na ƙwace filaye mallakar fararen fata ba bisa ƙa’ida ba.
Barazanar na zuwa ne yayin da a ƙarshen watan Janairun da ya gabata Shugaba Ramaphosa ya ƙaddamar da dokar da ta bai wa gwamnati damar ƙwace wasu filaye galibi mallakin fararen fata ba tare da biyan diyya ba a wani mataki na samar da daidaito da kuma adalci ga ’yan kasar.
Gwamnatin Afirka ta Kudu ta bayyana matakin a matsayin wani yunƙuri na gyaran kura-kurai na rashin daidaito da ƙasar ta gada daga Turawan mulkin mallakar na Birtaniya.
Sai dai wannan mataki ya gamu da suka daga masu ra’ayin mazan jiya ciki har da attajirin nan Elon Musk ɗan asalin Afrika ta Kudu wanda ke da kusanci da shugaba Donald Trump.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: wa Afirka ta Kudu
এছাড়াও পড়ুন:
Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
Shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar amfani da ƙarfin soji kan Najeriya matuƙar gwamnatin ƙasar ba ta dakatar da kisan da ’yan ta’adda masu iƙirarin jihadi ke yi wa Kiristoci ba.
A yammacin jiya Asabar ne Trump ya umarci Ma’aikatar Yaƙin Amurka ta Pentagon da ta soma tsara yadda za a kai hari Nijeriya bayan da ya yi zargin cewa ana yi wa Kiristoci kisan gilla a ƙasar.
Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Truth Social, Trump ya ce Amurka a shirye ta ke ta aike da sojoji da manyan makamai cikin Najeriya don bai wa Kiristocin kariya.
Barazanar shugaban na Amurka na zuwa ne kwana guda bayan ya yi iƙirarin cewa an kashe Kiristoci aƙalla 3,100 a Nijeriya ba tare da ya bayyana takamaimai inda ya samu waɗannan alƙaluma ba.
“Muddin gwamnatin Nijeriya ta ci gaba da bari ana kashe Kiristoci, Amurka za ta dakatar da dukkan tallafin da take bai wa Nijeriya nan-take, kuma mai yiwuwa za ta shiga wannan ƙasƙantacciyar ƙasar, cike da ƙarfin gwiwa domin kawar da ’yan ta’adda masu kaifin kishin Musulunci waɗanda ke yin wannan ta’asa,” in ji Trump.