Aminiya:
2025-09-17@23:28:28 GMT

An dakatar da dagaci kan zargin saran maraya da adda

Published: 8th, February 2025 GMT

An dakatar da Dagacin Karagawal da ke Jihar Gombe, Usman A. Bello, daga kujerarsa, har sai an kammala bincike kan zargin da ake masa na saran wani maraya da adda har sau bakwai.

A baya Aminiya ta ruwaito yadda jikin marayan, mai suna Adamu Muhammad mai shekara 15 ya fara ɗoyi saboda rashin samun kulawa bayan asibiti sun ƙi karbarsa saboda rashin kuɗi, sakamakon raunukan da yake zargin dagacin ya yi masa.

A yayin hirar da Aminiya ta yi da shi a lokacin, Dagacin ya musanta sarar yaron, inda ya bayyana cewa ya yi ƙoƙarin kare kansa ne bayan varayi ɗauke da makami sun shiga gidansa.

Lamarin da ya faru a farkon watan Disamba na shekarar 2024, wanda ya haifar da ce-cekuce a yankin.

‘A sansanin gudun hijira na yi sakandare har na zama likita’ Jirgin Amurka ɗauke da mutum 10 ya ɓace

Shugaban Ƙaramar Hukumar Gombe, Barista Sani A. A. Haruna, ya bayyana cewa an dakatar da basaraken ne domin tabbatar da adalci da kuma kare martabar duk wanda lamarin ya shafa.

Ya ce, “Mun ɗauki xawainiyar jinyar yaron, inda muka kashe sama da Naira dubu ɗari biyar. Wannan nauyi ne na gwamnati, ba iyayensa ba, domin ba shi ya ji wa kansa ciwo ba.”

Barista Haruna ya ce an dakatar da Dagacin ne bayan ƙorafin da aka samu cewa ya ɗauki matakin da ya saba wa doka, “ko da yaron ya aikata wani laifi, ba ya halatta a xauki doka a hannu. A maimakon haka, doka ta tanadi cewa a kai shi gidan horon yara. Amma abin da ya fi muhimmanci a yanzu shi ne tabbatar da cewa yaron ya samu sauqi kafin a ci gaba da bincike.”

Dagacin Karagawal, Usman A. Bello, ya kare kansa da cewar wasu matasa ne suka shiga gidansa da makamai cikin dare da nufin sata, wanda hakan ya sa shi ɗaukar matakin kare kansa.

Ya ce, “Na samu nasarar qwace adda daga ɗaya daga cikinsu, sannan na yi amfani da ita don kare kaina.’

A daya bangaren, saurayin aka yi wa raunin, Adamu Muhammad, ya musanta daukar makami ko aikata sata. Ya ce, “Na shiga gidan ne ba tare da izini ba, amma Dagacin ne ya zo da adda ya sassara ni har na ji ciwo a wurare daban-daban.”

Idan ba a manta ba, a baya yaron ya shaida wa wakilin Aminiya cewa ya je neman mafaka a gidan dagacin ne saboda tsoron matakin da mahaifiyarsa za ta xauka a kansa bayan ya yi faɗa da wata budurwa a makwabtansu, har ta kai ƙararsa wurin ’yan banga, suka nemi ya biya yarinyar kuɗi, kuma ba shi da su.

Shugaban ƙaramar hukumar ya ce za a gudanar da cikakken bincike ba tare da nuna son kai ba. Ya ce, “Ba za mu yanke hukunci yanzu ba, har sai mun saurari bayanin yaron da zarar ya samu lafiya.

“Idan aka yanke hukunci yanzu kuma daga baya wani abu ya taso, misali rashin lafiyarsa ko wani akasin haka, to shari’ar za ta canza gaba ɗaya.”

Ya kara da cewa matakin dakatar da Dagacin ya ba da damar gudanar da bincike cikin gaskiya da adalci. “Idan bincike ya tabbatar da cewa Dagacin ne ya yi wa yaron rashin adalci, to za a xauki matakin da ya dace. Idan kuma aka gano cewa yaron ne da laifi, za a yi hakan cikin tsari.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Karagwal

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya ta ce Najeriya na rasa sama da Dala Biliyan 10 duk shekara sakamakon asarar amfanin gona bayan girbi.

Ministan Noma  Sanata Abubakar Kyari ne ya bayyana haka a wajen kaddamar da shirin Hanyar Inganta Noma da Kayayyakin Mire Rayuwa a Yankunan Karkara G.R.A.I.N a ƙaramar hukumar Birnin Kudu ta  Jihar Jigawa.

 

Ya ce asarar na faruwa ne saboda rashin ingantattun wuraren ajiya, karancin ababen more rayuwa, sauyin yanayi da kuma ambaliya.

Kyari ya bayyana cewa noma na bada gudunmawar kashi 24 bisa 100 na Jimillar Darajar Kayayyaki da Ayyuka da Kasa ta Samar a Cikin Shekara GDP, inda ƙananan manoma ke samar da sama da kashi 70 bisa 100 na abincin da ake ci a ƙasa.

Ya jaddada cewa gwamnati za ta tallafa musu da kayan noma na  zamani da wuraran kasuwanci domin inganta tattalin arziki.

A nasa jawabin, Gwamna Umar Namadi na Jigawa ya yaba da samun Cibiyar Cigaban Karakara ta Pulse ta farko a Jigawa, yana mai cewa za ta kawo sauyi a harkar noma da rayuwar jama’ar karkara.

Haka zalika, shi ma Ministan Harkokin Waje, Yusuf Tuggar, ya ce haɗin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu zai taimaka wajen ci gaban tattalin arziki.

Shugaban ƙaramar hukumar Birnin Kudu, Alhaji Builder Muhammad Uba, ya jaddada goyon bayansa ga shirin Renewed Hope Agenda na Shugaba Tinubu tare da yabawa gwamnatin Namadi kan sauya fasalin noma a jihar.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza
  • Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Runduwar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar