Magungunan Jabu: ’Yan majalisa sun nemi yin hukuncin ɗaurin rai da rai
Published: 7th, February 2025 GMT
Majalisar Wakilan Tarayya ta buƙaci babban lauyan gwamnatin tarayya da ya gabatar da gyare-gyare ga dokokin da ake da su da nufin zartar da hukunci mai tsauri da suka haɗa da ɗaurin rai da rai ga waɗanda ke da hannu wajen sarrafawa da shigo da magungunan jabu.
Da kuma gaggarumin tara ga ’yan kasuwar da aka samu da laifin yin mu’amala da jabun kayayyaki.
Hakan ya biyo bayan wani ƙuduri kan muhimmancinsa ga jama’a da ɗan majalisa, Tolani Shagaya ya gabatar a zauren majalisar a ranar Alhamis.
Ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta kafa dokar ta-ɓaci kan barazanar rarrabawa da sayar da magunguna da kayayyakin abinci na jabu, marasa inganci ko waɗanda wa’adin aikin su ya ƙare a ƙasar.
Yayin da yake gabatar da ƙudirin a zauren majalisar, ya ce ƙaruwar sarrafa da shigo da kayayyaki na jabu da marasa inganci da magunguna da abinci da abubuwan sha a faɗin Najeriya na haifar da babbar barazana ga lafiyar al’umma, tsaron ƙasa da kuma tattalin arzikin ƙasa.
Ya ce, “Kwanan nan Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna a Najeriya NAFDAC ta kama jabun kayan abinci da magunguna da suka kai na sama da Naira biliyan 5 a wani samame da suka kai a kasuwar Cemetery Market da ke garin Aba, Jihar Abia lamarin da ya nuna yadda wannan matsalar ke yaduwa.
“Najeriya na fama da asarar tattalin arziki kusan tiriliyan 15 a duk shekara saboda jabun kayayyaki da marasa inganci, kamar yadda Hukumar Daidaita Ma’auni ta Najeriya (SON) ta ruwaito. Yaɗuwar samfuran jabu ba wai kawai yana kawo cikas ga amincin masu amfani ba har ma yana hana saka hannun jari na gaske a masana’antar abinci da magunguna.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Majalisar Wakilai Najeriya
এছাড়াও পড়ুন:
Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
Babban sakataren MDD António Guterres, ya bayyana a jiya Talata cewa, jerin shawarwarin da Sin ta gabatar wato shawarar raya duniya, shawarar tabbatar da tsaron duniya, shawarar raya wayewar kan al’ummun duniya, da kuma jagorantar harkokin duniya, sun dace da ka’idar kundin tsarin MDD.
Guterres ya bayyana hakan ne yayin da yake amsa tambayoyin ‘yan jarida a wani taron manema labarai da aka yi a ranar. Ya ce shawarwarin da Sin ta gabatar sun mutunta manufar kasancewar bangarori da dama, kuma sun goyi bayan MDD a matsayin cibiyar hadin gwiwar kasa da kasa, tare da dukufa kan inganta hadin gwiwa tsakanin kasashe daban daban da warware rikice-rikice cikin lumana.
Guterres ya kara da cewa, yanzu ana fuskantar rarrabuwar kawuna a fagen siyasa ta duniya da kuma karuwar yaduwar rikice-rikice, da ma rashin hukunta masu laifi. Bugu da kari, sabbin fasahohi suna ci gaba da bullowa “ba tare da bin wani tsari ba”, yayin da rashin daidaito ke kara tsananta. A wannan yanayi, babban taro karo na 80 na MDD mai tsawon mako guda da za a fara a mako mai zuwa, zai ba da duk wata dama ga tattaunawa da shiga tsakani.(Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp