Aminiya:
2025-06-18@02:54:39 GMT

Magungunan Jabu: ’Yan majalisa sun nemi yin hukuncin ɗaurin rai da rai

Published: 7th, February 2025 GMT

Majalisar Wakilan Tarayya ta buƙaci babban lauyan gwamnatin tarayya da ya gabatar da gyare-gyare ga dokokin da ake da su da nufin zartar da hukunci mai tsauri da suka haɗa da ɗaurin rai da rai ga waɗanda ke da hannu wajen sarrafawa da shigo da magungunan jabu.

Da kuma gaggarumin tara ga ’yan kasuwar da aka samu da laifin yin mu’amala da jabun kayayyaki.

’Yan bindiga sun mamaye masallaci da awon gaba da masallata a Sakkwato Lakurawa sun kashe mutum 1 sun jikkata 6 a Kebbi

Hakan ya biyo bayan wani ƙuduri kan muhimmancinsa ga jama’a da ɗan majalisa, Tolani Shagaya ya gabatar a zauren majalisar a ranar Alhamis.

Ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta kafa dokar ta-ɓaci kan barazanar rarrabawa da sayar da magunguna da kayayyakin abinci na jabu, marasa inganci ko waɗanda wa’adin aikin su ya ƙare a ƙasar.

Yayin da yake gabatar da ƙudirin a zauren majalisar, ya ce ƙaruwar sarrafa da shigo da kayayyaki na jabu da marasa inganci da magunguna da abinci da abubuwan sha a faɗin Najeriya na haifar da babbar barazana ga lafiyar al’umma, tsaron ƙasa da kuma tattalin arzikin ƙasa.

Ya ce, “Kwanan nan Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna a Najeriya NAFDAC ta kama jabun kayan abinci da magunguna da suka kai na sama da Naira biliyan 5 a wani samame da suka kai a kasuwar Cemetery Market da ke garin Aba, Jihar Abia lamarin da ya nuna yadda wannan matsalar ke yaduwa.

“Najeriya na fama da asarar tattalin arziki kusan tiriliyan 15 a duk shekara saboda jabun kayayyaki da marasa inganci, kamar yadda Hukumar Daidaita Ma’auni ta Najeriya (SON) ta ruwaito. Yaɗuwar samfuran jabu ba wai kawai yana kawo cikas ga amincin masu amfani ba har ma yana hana saka hannun jari na gaske a masana’antar abinci da magunguna.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Wakilai Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe

An fargabar cewa ’yan bindiga sun kashe akalla mutum 100 a wani hari da suka kai a garin Yelewata da ke yankin Karamar Hukumar Guma a Jihar Benuwe.

Aminiya ta ruwaito cewa maharan sun far ma al’ummar garin na Yelewata ne a cikin daren ranar Juma’a wayewar garin Asabar.

Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa

Wadanda suka shaida harin na Yelewata sun ce maharan sun mamayi garin ne kafin karfe 12 na dare, inda suka kwashe sama da sa’a biyu suna ta’annati ba tare da wani dauki daga jami’an tsaro ba.

Da yake zantawa da Kamfanin Dillancin Labarai na AFP, wani mai magana da yawun fadar gwamnatin Benuwe, Tersoo Kula, ya tabbatar da faruwar lamarin yana mai cewa maharan sun kone gidaje da dama.

Sai dai ya ce jami’an gwamnati da suka kai ziyara yankin na Yelwata sun samu cewa wadanda aka kashe ba su wuce mutum 45 ba.

Shi ma mai magana da yawun ’yan sandan jihar, Udeme Edet, ya ce jami’ansu sun yi musayar wuta da maharan.

Haka kuma, an wani harin na daban da ya auku an kashe sojoji biyu a garin Daudu, shi ma a yankin karamar hukumar ta Guma.

Wannan harin shi ne na uku a baya-bayan nan a garin Yelewata wanda ke kan iyakar jihar ta Benuwe da Nasarawa a cikin mako daya.

Ana iya tuna cewa a watan da ya gabata ne wasu mahara da ake zargin makiyaya ne suka kashe kimanin mutum 20 a karamar hukumar Gwer ta Yamma a jihar ta Benuwe.

Kungiyar Amnesty mai fafutikar kare hakkin dan Adam ta yi kira ga gwamnatin da ta dauki matakin dakile zubar jini da salwantar rayukan al’umma a kasar.

Amnesty ta ce gazawar gwamnatin Nijeriyar ce ta sanya asarar rayukan al’ummar kasar ta zama ruwan dare.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Ya Gabatar Da Muhimmin Jawabi A Taron Koli Na Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu
  • Tankokin Isra’ila sun kashe mutum 51 a wurin karbar abinci a Gaza
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Cin Ganyayyaki Ke Yi Wa ‘Yan Najeriya Wahala
  • An Zartar Da Hukuncin Kisa Kan Dan Leken Asirin Haramtacciyar Kasar Isra’ila A Iran
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Durƙushewar Sababbin Sana’o’i Tun Ba A Je Ko’ina Ba
  • An tallafa wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a Kaduna
  • Cece-Kuce Ya Barke Bayan Ganduje Da Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas Sun Nemi A Sauya Shettima A 2027
  • APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu
  • Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensa
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe