An Fara Binciken Badaƙalar Haɗa NIN-SIM Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Published: 7th, February 2025 GMT
Majalisar wakilai ta umarci kwamitocin sadarwa da harkokin cikin gida da su binciki haɗa lambar shaidar zama ɗan ƙasa (NIN) da layukan waya ba tare da izini ba da kamfanonin sadarwa ke yi.
Wannan mataki ya biyo bayan ƙudirin da ‘yan majalisa Patrick Umoh da Julius Ihonvbere suka gabatar, inda aka buƙaci hukumar NCC ta ɗauki mataki kan duk wani kamfanin sadarwa da aka samu da laifi, tare da NIMC ta tabbatar da sahihancin haɗa bayanan NIN.
Umoh ya ce wannan mataki na iya haifar da damuwa ga ‘yan ƙasa, tare da jefa su cikin hatsarin satar bayanai, da damfara, da wasu laifukan intanet. Kwamitin binciken na da makonni huɗu domin kammala aikinsa.
এছাড়াও পড়ুন:
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba
Wannan ya janyo tambayoyi kan ko za ta iya komawa nan take.
A lokacin da aka tambaye ta me take yi a lokacin da aka dakatar da ita, Sanata Natasha ta ce ba ta tsaya ba, har yanzu tana gudanar da ayyuka tare da wakiltar mutanenta.
“Na kasance ina aiki a duk lokacin. Na ci gaba da aiki kuma ina shirin gabatar da wasu dokoki a kan ma’adanai. Ba zan iya miƙa su ga wani ba,” in ji ta.
Ta ƙara da cewa duk da cewa ba ta halartar zaman majalisa, ta ci gaba da yin ayyukan ci gaba ga mutanenta.
“Fitar da ni daga majalisa ba kawai ni aka daƙile ba, an hana muryar Kogi ta Tsakiya fitowa fili,” in ji ta.
“Majalisar Dattawa ta hana mata da yara ‘yan Nijeriya samjn wakilci. Yanzu muna da Sanata mata guda uku kacal, alhali a baya muna da takwas.”
LEADERSHIP ta ruwaito cewa sanarwar dawowarta da aka shirya yi a ranar Talata ta tayar da hankula a majalisar, inda aka tsaurara tsaro kuma aka kawo motocin jami’an tsaro da dama.
Shige da fice daga harabar majalisar ya kasance a ƙarƙashin kulawar jami’an tsaro, inda ake bincikar motoci kafin ba su iznin shiga.
Ko da yake ba ta koma majalisar ba tukuna, Sanata Natasha ta jaddada cewa za ta ci gaba da yin aikinta.
“Ina da niyyar ci gaba da wakiltar Kogi ta Tsakiya da Nijeriya gaba ɗaya,” in ji ta.
“Ko na je majalisa ko ban je ba, zan ci gaba da sauke nauyin da ke kaina.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp