Ministan Yakin HKI Ya Bada Umurnin A Fidda Tsarin Falasdinawa Daga Gaza Da Zabin Kansu
Published: 7th, February 2025 GMT
Ministan yaki na HKI Israel Kant ya umurci jami’an gwamnatin kasar su fidda wani tsari wanda zai bawa falasdinawa damar ficewa daga yankin Gaza a radin kansu.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ministan ya na haka bi sa umurnin da shugaba Trump na Amurka ya bayar na cewa ‘zai kwace Gaza’.
Shugaban kasar Amurka yace ya dauki nauyin fidda Falasdinawa daga gaza, don wurin ya zama na yahudawan sahyoniyya kadai.
Wasu masana suna ganin mai yuwa wannan shirin zai kawo karshen zaman lafiyan da aka samu, bayan yaki na watanni 15 da suka gabata.
Kant ya bukaci tsarin ya kasance, kan cewa falasdinawa a Gaza za su fice daga gaza su je ko ina suke a duniya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Wasu al’ummomi sun bayyana dalilan da suka sa suka karbi tsarin yin gwajin lafiyar ma’aurata kafin a daura musu aure.
A wasu lokutan, akan samu matsaloli sakamakon rashin gwajin jini kafin a hada mace da na miji aure. Matsalolin sun hada da yaduwar cututtuka, samun ‘ya’ya marasa lafiya da sauran wasu matsalolin.
NAJERIYA A YAU: Yadda Za A Dama Da Matan Arewa A Fannin Kimiyya DAGA LARABA: Abubuwan da ya kamata yara su yi yayin hutun makarantaShirin Daga Laraba na wannan makon zai yi nazari ne kan dalilan da suka sa wasu alummomin suka rungumi yin gwajin jini kafin aure.
Domin sauke shirin, latsa nan