Aminiya:
2025-06-16@04:19:39 GMT

An tsinci gawar Ɗan Majalisar da aka yi garkuwa a jajibirin Kirsimeti

Published: 6th, February 2025 GMT

An tsinci gawar mai shari’a Azuka, Ɗan Majalisa mai wakiltar mazaɓar Onitsha ta Arewa a Majalisar Dokokin Jihar Anambra.

An gano gawar Azuka da aka sace a jajibirin Kirsimeti a shekarar 2024 a kan gadar 2nd Niger Bridge, a cikin Anambra, ranar Alhamis.

Uwa ta fusata ta jefa ’yarta cikin kogi a Bayelsa Yadda matar aure ta kashe dan kishiyarta da tafasasshen ruwa

Marigayin yana hanyarsa ta zuwa bukukuwan ƙarshen shekara ne tare da ‘yan uwansa a lokacin da ’yan bindiga suka yi awon gaba da shi a Ugwunakpamkpa da ke cikin garin Onitsha.

Sai dai jami’an tsaro da ke binciken sace shi sun cafke wasu da ake zargin sun kai su inda aka gano gawarwakin mambobin jam’iyyar Leba.

Da aka tuntuɓi jami’in hulɗa da jama’a na ’yan sanda a Anambra, SP Tochukwu Ikenga, ya tabbatar da faruwar lamarin.

“Jami’anmu sun gano gawar yanzu. Kuma ina ganin ya kamata su kasance a kan hanyarsu a yanzu su kawo gawar nan (hedkwatar ’yan sandan jihar, Amawbia). Za mu sanar da manema labarai da zarar gawar ta iso nan,” in ji SP Ikenga

Da aka tambaye shi ya ba da cikakken bayani kan yadda aka gano gawar, sai ya ce, “Ina son Kwamishanan ‘yan sanda ya yi magana a kai. Ku jira kawai, zai yi wa manema labarai bayani a kai.”

Azuka shi ne ɗan majalisa a karo na biyu da aka kashe a Anambra a cikin shekaru biyu da suka gabata.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Anambra Majalisar Dokokin Jihar

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin da muka soke tattaunawar nukiliya da Amurka — Iran

Iran ta sanar da soke zaman tattaunawa da ya kamata ta yi da Amurka kan batun nikiliyarta a Oman yau Lahadi saka makon hare-haren da Isra’ila ta kai mata a ranar Juma’a.

Bayanai sun ce a wannan Lahadin ce ya kamata a gudanar da ganawa ta shida tsakanin wakilan Amurka da na Iran a birnin Musqat na Oman.

Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe

Sai dai kakakin Ministan harkokin wajen Iran, Esmaeil Baqaei ya bayyana cikin wata sanarwa cewa, Amurka ta nuna fuska biyu, inda a gefe guda take tattaunawar cimma masalahar jingine ƙera nukiliya da Iran, amma a ɗaya gefen kuma ta goyi bayan harin da Isra’ila ta kai mata.

Iran ta zargi Amurka da goyon bayan harin da Isra’ila ta kai mata, sannan kuma ta ce tattaunawar yarjejeniyar dakatar da ƙera makamin ƙare dangi na nukiliya da take yi da Amurkar ba ta da wani amfani.

A nasa ɓangaren, Ministan harakokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya ce babu buƙatar ci gaba da tattaunawa da aka faro tsakiyar watan Afirilun wannan shekara lura da harin dabbanci da Isra’ila ta kai mata.

Kafofin yaɗa labarai da dama a Iran sun shaida cewa guda daga cikin masu baiwa jagoran addinin musluncin Iran ayatoAllah Ali Khamenei kuma mai taka muhimmiyar rawa a tattaunawar, Ali Shamkhani, na daga cikin waɗanda su ka ji rauni a hare-haren na Isra’ila.

Tun farko Isra’ila ce ta fara kai wa Iran hari kan cibiyoyin nukiliyarta tare da halaka manyan hafsoshin tsaronta, cikin daren Alhamis zuwa wayewar garin Juma’a, kuma ta ci gaba da kai farmaki da makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa, mafarin buɗe kofar wani sabon rikici a tsakanin ƙasashen biyu da suka jima suna adawa da juna tsawon shekaru.

Harin ramuwar gayya da Iran ta kai wa Isra’ila da safiyar Asabar ya halaka mutane uku, tare da jikkata wasu da dama a biranen Jerusalem da Tel Aviv, inda hukumomin Isra’ila ke ci gaba da gargaɗin ‘yan kasar su nemi mafaka.

A wani jawabi da jagoran addini na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya gabatarwa al’ummar kasar ranar Juma’a, ya ce ba za su saurara wa Isra’ila ba sakamakon munin abin da ta aikata musu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dan Asalin Tudun Loess
  • Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
  • Dalilin da muka soke tattaunawar nukiliya da Amurka — Iran
  • Kula Da Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawa guda bayan kwanaki 8
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
  • Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje