Aminiya:
2025-07-31@08:13:06 GMT

Uwa ta fusata ta jefa ’yarta cikin kogi a Bayelsa

Published: 6th, February 2025 GMT

A wani rahoto na ibtila’i da ya afku a unguwar Ukubie da ke ƙaramar hukumar Ijaw ta Kudu a Jihar Bayelsa inda wata mata mai suna Madam Stella ta jefa ‘yarta ’yar shekara shida mai suna Rachael a cikin kogi saboda fushi.

A cewar shaidu, Rachael ta je yin wanka a bakin kogi duk da gargaɗin da mahaifiyarta ta yi mata.

Yadda matar aure ta kashe dan kishiyarta da tafasasshen ruwa An sace tsohon Shugaban Hukumar NYSC, Janar Tsiga

“Lokacin da mahaifiyar ta samu ’yarta a bakin kogin, sai ta fusata. Duk da gargaɗin da aka yi mata na ƙauracewa kogin, Rachael ta ƙi, wanda hakan ya sa mahaifiyar tashin hankali ta fusata,” in ji wani ganau.

A cikin fushi, an samu rahoton cewa Madam Stella ta kama hannun Rachael kuma ta jefa ta a cikin wuri mai zurfi a kogin sau biyu, wanda ya kai ga mutuwar ‘yarta.

Bayan faruwar lamarin, jama’ar yankin unguwar da abin ya shafa sun tunkari mahaifiyar, inda ta amsa aikata laifinta, inda ta ce ba ta yi niyyar kashe ɗiyarta ba.

Lamarin da ya jefa jama’ar yankin Ukubie cikin firgici, inda wani ɗan uwansu mai suna Jeph Nation ya bayyana ra’ayinsa.

“Na riga na rasa ‘yan uwa guda biyu a wannan shekara, amma wannan shi ne mafi zafi da ban tausayi,” in ji shi.

Hotunan bidiyo da ke yawo a shafukan sada zumunta sun nuna Madam Stella ta furta wannan iƙirari da yaren ƙabilar Ijaw, inda jama’a suka kewaye ta.

A wani  bidiyo, an ganta zaune a cikin kwale-kwale da gawar ɗiyarta a gefenta, tana ɗauke da ita.

A halin da ake ciki, rundunar ‘yan sandan Jihar Bayelsa, ta bakin kakakinta, DSP Musa Mohammed, ya bayyana cewa har yanzu ba a kai ga sanar da rahoton faruwar lamarin ga ‘yan sanda ba a hukumance.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bayelsa Ijaw Mahaifiya

এছাড়াও পড়ুন:

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

Ya bayyana halin da aka shiga mara daɗi, inda ya jajanta wa iyalan waɗanda suka mutu da waɗanda suka yi asarar dukiyoyi, yana mai tabbatar da cewa gwamnati za ta tallafa musu wajen sake gina musu gidajen su da sauya muhallinsu.

Fintiri ya kuma soki waɗanda ke yaɗa rahotannin ƙaryar game da lamarin, ba tare da fahimtar ainihin abin da ke faruwa ba, inda ya ce hakan yana da nasaba da tuggun siyasa da son zuciya.

Ya bayyana cewa maƙasudin ambaliyar sun haɗa da ruwan sama mai yawa da toshewar hanyoyin ruwa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Mamakon ruwan sama ya haddasa ambaliya a Maiduguri 
  • Majalisa ta ba NNPCL mako uku ya yi mata bayanin inda tirilyan 210 ta shiga
  • ’Yan bindiga sun tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
  • ’Yan sa-kai aƙalla 100 da jami’an tsaro 30 sun mutu a bakin aiki a Katsina —Gwamnati
  • Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
  • Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar
  • Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyar Mutuwar Mutane Da Dama A Yola