Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci A Iran Ya Sanya Sheikh Na’im Kasim A Matsayin My Wakiltarsa A Kasar Lebanon
Published: 6th, February 2025 GMT
A wani umurnin da ya bayar Jagoran juyin juya halin musulunci a nan Iran, Imam Aya. Sayyid Alilul Khami’nae ya sanya babban sakataren kungiyar Hizbullah a matsayin wakilinsa a kasar Lebanon.
Bayan shahadar Sayyed Hassan Nasarallah da kuma Sayyed Hashim safiyuddeen An zabi sheikh Na’em Kasim a matsayin babban sakataren kungiyar ta Hizbullah a kasar Lebanon.
Sheikh Qasim dai ya taka rawar a zo a gani wajen yakin da kungiyarsa ta shiga da HKI na watanni 15.. Kuma ana saran shi ne zai zama mai fitar da kungiyar zuwa tudun na tsira daga halin da ta shiga ciki ya kuma ci gaba da yakar kungiyar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bude Kofofin Jahannama Ga Yahudawan Sahayoniyya
Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta bude kofofin wuta a kan haramtacciyar kasar Isra’ila ta hanyar mayar da martani kan harin da yahudawan sahayoniyya suka kai kan kasarta
Iran ta bude kofofin jahannama kan ‘yan sahayoniyya a matsayin mayar da martani ga mummunan zaluncin da suka kaddamar kan lardunan Iran da dama, wanda ya yi sanadiyyar shahadan mutane da dama da jikkata.
Bayan da Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya jaddada cewa: Wajibi ne gwamnatin mamayar Isra’ila ta jira mummunan hukunci mai tsanani da kuma makoma mai daci kan abin da aikata, kuma bayan da sabon kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci Manjo Janar Muhammad Pakpour ya bayyana cewa: Sojojin kasar Iran za su bude kofofin jahannama kan kisan yara kanana, Iran ta fara kaddamar da hare-haren daukan fansa mai suna “Alkawarin Gaskiya na 3”, inda ta harba makamai masu linzami na ballistic da hypersonic kan yankuna daban daban na haramtacciyar kasar Isra’ila.
A cewar faifan bidiyo da aka wallafa, hakika Iran ta kai hare-hare da makamai masu linzami kan tsakiyar birnin Tel Aviv da kuma cibiyoyi da dama na soji da sansanonin sojin saman haramtacciyar kasar Isra’ila.