“Canada, Mexico da Sin su ne suke sayen rabin duk kayayyakin amfanin gona da Amurka ke fitarwa. Kasuwanni ne da muke bukata babu makawa don raya tattalin arzikin Amurka. Sanya haraji kan manyan kasuwannin fitar da kayayyakin guda uku na noma da kiwo na Amurka, musamman na dogon lokaci zai haifar da mummunan sakamako,” in ji sanarwar.

Tabbas! abin da manoman suka fada gaskiya ne, domin ko a shekarar 2018, karin harajin da Amurka ta kakkaba a kan kayayyakin kasar Sin, ya janyo kasar ta Sin wadda a baya ita ce ta fi shigo da wake na Amurka, ta sanya karin harajin kashi 25 cikin 100 na ramuwar gayya kan kayayyakin da Amurka ke fitarwa. Kuma a yanzu ma, Sin ta lashi takobin mayar da martani inda tuni, a farkon makon nan ta fitar da sanarwa daga ma’aikatar cinikayya da ma’aikatar kudi a kan fara aiwatar da martaninta ga Amurka.

Daga ciki, kasar Sin ta sanya harajin kashi 10% zuwa 15% kan wasu kayayyakin da ake shigowa da su daga Amurka, wanda zai fara aiki daga ranar 10 ga Fabrairun nan. Sannan, Sin ta yanke shawarar shigar da rukunin kamfanonin US PVH da Illumina a cikin jerin kamfanonin da ba su da tabbas. Kana ta shigar da kara a gaban Kungiyar Kasuwanci ta Duniya, watau WTO. Bugu da kari, Sin ta hana fitar da wasu sinadarai masu muhimmanci da ake amfani da su wajen hada kayayyakin lantarki da na karafa.

Fitina dai a kwance take, kuma la’ana tana kan duk wanda ya tayar da ita! (Daga Abdulrazaq Yahuza Jere)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai

Wasu Hare-haren da gwamnatin Isra’ila ta kai ya haddasa gobara a wasu matatun mai a lardin Bushehr da ke kudancin kasar Iran.

Gobarar ta tashi ne a wurin a ranar Asabar bayan da wasu kananan jiragen yakin Isra’ila guda biyu suka kai hare-hare a kan kayayyakin sarrafa iskar gas da ke yankin kudancin Pars.

Hare-haren sun yi haddassa fashe fashe a matatar iskar gas ta Fajr-e Jam, daya daga cikin mafi girma a Iran, da kuma wata karamar matatar mai a mataki na 14 na tashar iskar gas ta Kudu Pars.

Har yanzu ba a fitar da kiyasin barnar a hukumance ba.

Bayan gobarar, ma’aikatar mai ta Iran ta fitar da wata sanarwa inda ta tabbatar da harin.

Sanarwar ta ce, nan da nan aka kaddamar da aikin shawo kan gobarar da dakile ta.”

Matatar man ta Pars ta kudu ita ce tashar iskar gas mafi girma a duniya, wacce ke kan iyakar teku tsakanin Iran da Qatar.

Ta kunshi sama da kashi 70% na bukatun iskar gas na Iran.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAF Na Shirin Siyo Jiragen Yaki Masu Saukar Ungulu Daga Amurka
  • Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
  • An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai
  • Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka
  • Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba
  • Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa
  • Jagoran Juyin Musulunci Na Iran Ya Nada Sabbin Kwamandojin Soja Da Dakarun Kare Juyin Musulunci
  • Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi
  • Leroy Sane ya koma Galatasaray
  • Iran ta caccaki kudurin IAEA wanda ta ce yana cike da siyasa