Aminiya:
2025-09-17@23:24:30 GMT

Yau Majalisar za ta ci gaba da aiki kan Dokar Haraji

Published: 4th, February 2025 GMT

A Talatar nan Majalisar Dokoki ta kasa ta ci gaba zama don hanzarta kammala aiki kan ƙudirin sabuwar dokar haraji mai cike da ruɗani da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gabatar mata.

Bayan zaman farko a ranar 14 da watan nan na Janairu, ta dage zama zuwa ranar 28 domin kwamitoci su kammala aikin tantance kasafin 2025, amma daga bisani ta sake dage zuwa 4 ga Fabrairu domin kwamitocinta su gama sauraron kare kasafin hukumomin gwamnati.

Kafin tafiyar majalisar hutu, an tayar da jijiyoyin a Najeriya kan wasu dokoki hudu na haraji da Shugaba Tinubu ya gabatar wa Majalisar a ranar 13 ga Oktoban 2024.

Gwamnoni da sauran masu ruwa da tsaki na yankin Arewa na zargin dokokoin da nufin danniya da neman talauta yankin, inda suka bukaci a soke dokar.

Amma daga bisani bayan zaman da kungiyar gwamnoni ta kasa (NGF) da Kwamitin Shugaban Kasa kan dokar harajin, aka samu daidaito inda masu adawa da ita suka mayar da wukakensu cikin kube.

Daga cikin matsayar da suka cimma akwai rabon kashi 30% na kudaden harajin sayen kayayyaki (VAT) ga jihohin da aka sayi kayan, maimakon 60% da Tinubu ya nema.

Sun kuma amince da raba 50% na VAT daidai a tsakanin duk jihohi, ragowar 20% kuma gwargwadon yawan al’ummar kowace jiha domin tabbatar da adalci.

Bayan nan ne Gwamna Abdullahi Sule na Jihar Nasarawa ya ce za su nemi goyon bayan ’yan majalisar dokoki ta kasa daga jihohinsu domin ganin dokar ta samu shiga.

Wakilinmu ya ruwaito cewa masu ruwa da tsaki, ciki har da wasu gwamnoni sun kasa sun tsare domin ganin yadda za ta kaya a Majalisar Dokoki ta Kasa kan lamarin dokar mai cike da rudani.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arewa Dokar Haraji

এছাড়াও পড়ুন:

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

A bayan bayan nan, an aiwatar da jerin tattaunawa tsakanin Sin da Amurka karkashin jagorancin shugabanninsu, inda aka samu kyawawan sakamakon da ya kyautata alakarsu ta tattalin arziki da cinikayya. Wannan ya nuna shawarar da a kullum Sin ke bayarwa cewa, tattaunawa ita ce mafita ga dukkan rikice-rikice, maimakon amfani da karfi.

Kasar Sin ta sha nanata cewa, babu mai samun nasara a yakin cinikayya ko haraji. Mun ga yadda aka samu hauhawar farashin kayayyaki da karuwar rashin aikin yi da faduwar darajar hannayen jari a Amurka, a lokacin da ta kaddamar da yakin haraji, wanda ya nuna cewa, maimakon cimma abun da take fata na samun fifiko, asara aka samu da lalacewar muradun kamfanoni da ’yan kasuwar kasar.

Kowace kasa tana da cikakken iko da ’yancin zabar manufofi da matakan da ya dace da ita. Da Sin ta tsaya kai da fata cewa ba za ta ba da kai a yakin haraji da Amurka ta tayar ba, hakan ya sa Amurka yin karatun ta nutsu, kuma ta tuntubi bangaren Sin domin tattaunawa.

Wadannan misalai sun nuna mana cewa, akwai hanyoyi masu sauki da inganci na samun maslaha, kuma shawarwarin da Sin take gabatarwa, su ne suka dace da yanayin duniya a yanzu. Ba dole sai kowa ya samu abun da yake so ba, amma hawa teburin sulhu da tuntubar juna tana taka muhimmiyar rawa wajen warware sabani, da lalubo inda kowane bangare zai iya saki, domin a samu mafitar da za ta karbu ga kowa. Kuma irin wannan din, shi ne burin sabuwar Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya da shugaban kasar Sin ya gabatar a baya bayan nan. Duniya ba ta bukatar mayar da hannu agogo baya ta hanyar tayar da rikice-rikice da danniya da nuna fin karfi, zamani ya sauya kuma dole salon tafiyar da harkoki ya sauya, domin dacewa da yanayin da ake ciki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas
  • Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja