Yau Majalisar za ta ci gaba da aiki kan Dokar Haraji
Published: 4th, February 2025 GMT
A Talatar nan Majalisar Dokoki ta kasa ta ci gaba zama don hanzarta kammala aiki kan ƙudirin sabuwar dokar haraji mai cike da ruɗani da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gabatar mata.
Bayan zaman farko a ranar 14 da watan nan na Janairu, ta dage zama zuwa ranar 28 domin kwamitoci su kammala aikin tantance kasafin 2025, amma daga bisani ta sake dage zuwa 4 ga Fabrairu domin kwamitocinta su gama sauraron kare kasafin hukumomin gwamnati.
Kafin tafiyar majalisar hutu, an tayar da jijiyoyin a Najeriya kan wasu dokoki hudu na haraji da Shugaba Tinubu ya gabatar wa Majalisar a ranar 13 ga Oktoban 2024.
Gwamnoni da sauran masu ruwa da tsaki na yankin Arewa na zargin dokokoin da nufin danniya da neman talauta yankin, inda suka bukaci a soke dokar.
Amma daga bisani bayan zaman da kungiyar gwamnoni ta kasa (NGF) da Kwamitin Shugaban Kasa kan dokar harajin, aka samu daidaito inda masu adawa da ita suka mayar da wukakensu cikin kube.
Daga cikin matsayar da suka cimma akwai rabon kashi 30% na kudaden harajin sayen kayayyaki (VAT) ga jihohin da aka sayi kayan, maimakon 60% da Tinubu ya nema.
Sun kuma amince da raba 50% na VAT daidai a tsakanin duk jihohi, ragowar 20% kuma gwargwadon yawan al’ummar kowace jiha domin tabbatar da adalci.
Bayan nan ne Gwamna Abdullahi Sule na Jihar Nasarawa ya ce za su nemi goyon bayan ’yan majalisar dokoki ta kasa daga jihohinsu domin ganin dokar ta samu shiga.
Wakilinmu ya ruwaito cewa masu ruwa da tsaki, ciki har da wasu gwamnoni sun kasa sun tsare domin ganin yadda za ta kaya a Majalisar Dokoki ta Kasa kan lamarin dokar mai cike da rudani.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Arewa Dokar Haraji
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya ta ayyana hutu gobe Alhamis
Gwamnatin Nijeriya ta ayyana gobe Alhamis 1 ga watan Mayu a matsayin ranar hutu ga ma’aikatan ƙasar albarkacin bikin murnar Ranar Ma’aikata ta Duniya.
Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da Ministan Harkokin Cikin Gida na ƙasar, Olubunmi Tunji-Ojo, ya fitar a yammacin wannan Larabar.
AU ta janye takunkumin da ta ƙaƙaba wa Gabon Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsuSanarwar ta ambato ministan yana yaba wa ma’aikatan ƙasar kan sadaukarwa da jajircewar da suke yi wajen gudanar da ayyukansu.
Ministan ya kuma yaba musu kan gudunmawar da suke bayarwa wajen ciyar da Nijeriya gaba.
Ana dai gudanar da bikin Ranar Ma’aikata a ranar 1 ga watan Mayun kowace shekara a sassan duniya.