Tshohon daractan hukumar kare hakkin bil’ada ta MDD Craig Mokhiber ya yi kira ga Amurkawa su dawo daga rakiyar gwamnatin Trump da kuma firai ministan HKI Benyamin Natanyahu, mashayin jinin Falasdiwa, a dai dai lokacinda yake ziyararsa ta farko zuwa kasar Amurka tun bayan da Trump ya sake dawowa fadar White House.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Craig Mokhiber ya na fadar haka a shafinsa na X a jiya litinin, ya kuma kara da cewa, irin tarban da gwamnatin Trump ta bawa Natanyahu, da kuma yadda wasu yan majalisar dokokin kasar suka himmatu, ya nuna cewa babu bambanci a tsakanin gwamnatin Joe Biden da kuma Trump idan an yi maganar dangantar Amurka da HKI.

Yace dukaninsu mashaya jinin Falasdinawa ne, kuma sune suke gudanar da harkokin shugabancin Amurka a bayan fage. Banda haka su ne wadanda suke da biliyoyin dalar Amurka wadanda suke jujjuya duniya da su.  

Yace: Amurka ta kara tallafin da take bawa HKI daga dalar biliyon 03 zuwa dalar biliyon 24 a wannan shekara wanda ya nuna cewa zasu ci gaba da yaki da kuma zubar da jin Larabawa ne fiye da kisan kiyashin da suka yi watani 15 da suka gabata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutumin Da Ake Tuhuma Da Safarar Miyagun Kwayoyi

A kokarinsa na gano hakikanin dalilan da suka sa aka bayar da beli ga wani sanannen mai safarar miyagun kwayoyi, Sulaiman Aminu Dan Wawu, da aka ce an sako shi bisa umarnin Kwamishinan Sufuri na Kano, Ibrahim Ali Namadi, Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya kaddamar da wani kwamiti na mutum takwas domin gudanar da bincike mai zurfi.

Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Alhaji Umar Faruk Ibrahim ne ya kaddamar da kwamitin a madadin gwamnan.

An umurci kwamitin da ya gudanar da binciken cikin mako guda, domin gano hakikanin abin da ya faru da kuma ba da shawarwari kan matakin da ya dace a dauka.

Shugaban kwamitin shi ne Mai Bai wa Gwamna Shawara kan Harkokin Shari’a da Dokoki, Barista Aminu Hussaini, yayin da Mambobin kwamitin suka hada da Barista Hamza Haladu, Barista Hamza Nuhu Dantani, Darakta Janar na Hukumar Ayyuka na Musamman, Manjo Janar Muhammad Sani (rtd), Comrade Kabiru Dakata, da Farfesa Mamun Mustapha daga Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Dangote da ke Wudil.

Sauran mambobin sun hada da Alhaji Abdullahi Mahmud Umar, Kwamishina II na Hukumar Kula da Ma’aikata, da Hajiya Bilkisu Shehu Mai Mota, Babbar Sakatariya a Sashen Gudanarwa da Sauran Ayyuka na  ofishin Sakataren Gwamnatin .Jihar, wadda za ta rike matsayin Sakatariya ga kwamitin.

Gwamna Yusuf ya bayyana damuwarsa matuka kan zargin da ake yi, inda ya sake jaddada kudirinsa na yaki da safarar miyagun kwayoyi da duk wani nau’in barna a cikin al’umma.

Sakataren Gwamnatin Jihar ya bayyana kwarin gwiwarsa kan mambobin kwamitin, yana mai cewa an zabo su ne bisa cancanta, kwarewa, karsashi, da kuma kwarin gwiwar cewa za su gudanar da wannan aiki yadda ya kamata.

 

Abdullahi Jalaluddeen

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACF
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
  • Gwamnatin Kano Ta Kammala Gyaran Makarantu Sama Da 1,200 A Kananan Hukumomi 44
  • Gwamnatin Zamfara ta amince da naɗin sabon Sarkin Katsinan Gusau
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
  • Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata 
  • Rasha Ta Mayar Da Martani Ga Shugaban Amurka Kan Gindaya Wa’adin Kawo Karshen Yakin Ukraine
  • Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutumin Da Ake Tuhuma Da Safarar Miyagun Kwayoyi
  • Amurka Ta Dakatar Da Bai Wa ‘Yan Kasar Nijar Bisa Shiga Cikin Kasarta