Hajjin 2023: An dawo wa mahajjata 3,000 kuɗaɗensu a Kaduna
Published: 3rd, February 2025 GMT
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kaduna, ta bayyana cewa sama da mahajjata 3,000 da suka yi aikin Hajjin 2023 sun karɓi ragowar kuɗinsu da ya yi saura.
Mai magana da yawun hukumar, Malam Yunusa Abdullahi ne, ya bayyana hakancikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar a Kaduna.
’Yan sanda sun ceto mutum 23 da aka sace a Kaduna Arsenal ta yi sukuwar salla a kan Man City da ci 5Ya ce hukumar ta karɓo kuɗaɗen daga Hukumar Hajji ta Ƙasa (NAHCON).
Ya ce kowanne mahajjaci ya samu Naira 61,080.
Ya kuma ce an tura wa kuowa kuɗinsa kai-tsaye zuwa asusun bakinsu.
“NAHCON ta mayar da waɗannan kuɗaɗen ne saboda matsalar katsewar wutar lantarki da ta faru a Mina, wanda ya shafi sanyaya wuraren kwana kuma ya haifar wa mahajjata tsaiko,” in ji shi.
Abdullahi, ya ce akwai wasu da ba su karɓi kuɗinsu ba saboda rashin bayar da cikakkun bayanan asusun bankinsu.
Ya bayyana cewa biyan zagaye na biyu zai fara a mako mai zuwa, don haka ya buƙaci waɗanda ba su karɓi kuɗinsu ba da su gaggauta bahar da cikakken bayani domin samun kuɗinsu a kan lokaci.
Ya kuma jaddada cewa dukkanin mahajjatan 2023 da ba su karɓi kuɗinsu ba, su tuntubi jami’an rajista a ofisoshin ƙananan hukumominsu domin ƙarin bayani.
Hakazalika, ya ce yayin da ake ci gaba da biyankuɗaɗen na 2023, hukumar ta fara shirye-shiryen aikin Hajjin bana.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: ɗauke wuta
এছাড়াও পড়ুন:
Tsohon Ɗan Takarar Mataimakin Gwamnan Kaduna Na PDP Ya Koma ADC
Sai dai ya gode wa PDP bisa damar da ta ba shi ya tsaya takara a 2023, amma yanzu lokaci ya yi ne da zai yi gaba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp