Aminiya:
2025-09-17@22:19:45 GMT

Hajjin 2023: An dawo wa mahajjata 3,000 kuɗaɗensu a Kaduna

Published: 3rd, February 2025 GMT

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kaduna, ta bayyana cewa sama da mahajjata 3,000 da suka yi aikin Hajjin 2023 sun karɓi ragowar kuɗinsu da ya yi saura.

Mai magana da yawun hukumar, Malam Yunusa Abdullahi ne, ya bayyana hakancikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar a Kaduna.

’Yan sanda sun ceto mutum 23 da aka sace a Kaduna Arsenal ta yi sukuwar salla a kan Man City da ci 5

Ya ce hukumar ta karɓo kuɗaɗen daga Hukumar Hajji ta Ƙasa (NAHCON).

Ya ce kowanne mahajjaci ya samu Naira 61,080.

Ya kuma ce an tura wa kuowa kuɗinsa kai-tsaye zuwa asusun bakinsu.

“NAHCON ta mayar da waɗannan kuɗaɗen ne saboda matsalar katsewar wutar lantarki da ta faru a Mina, wanda ya shafi sanyaya wuraren kwana kuma ya haifar wa mahajjata tsaiko,” in ji shi.

Abdullahi, ya ce akwai wasu da ba su karɓi kuɗinsu ba saboda rashin bayar da cikakkun bayanan asusun bankinsu.

Ya bayyana cewa biyan zagaye na biyu zai fara a mako mai zuwa, don haka ya buƙaci waɗanda ba su karɓi kuɗinsu ba da su gaggauta bahar da cikakken bayani domin samun kuɗinsu a kan lokaci.

Ya kuma jaddada cewa dukkanin mahajjatan 2023 da ba su karɓi kuɗinsu ba, su tuntubi jami’an rajista a ofisoshin ƙananan hukumominsu domin ƙarin bayani.

Hakazalika, ya ce yayin da ake ci gaba da biyankuɗaɗen na 2023, hukumar ta fara shirye-shiryen aikin Hajjin bana.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: ɗauke wuta

এছাড়াও পড়ুন:

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Hukumar NDLEA ta bayyana cewa wata ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi ce a filin jirgin sama na Kano ta boye jakunkunan ƙwayoyi a cikin kayan matafiyan.

An kama shugaban ƙungiyar, Ali Abubakar Mohammed (wanda aka fi sani da Bello Karama), tare da wasu abokan aikinsa.

Hukumar ta ce mutanen ukun ba su da laifi kuma an zalunce su ne kawai.

An saki su ne bayan bincike da kuma ƙoƙarin diflomasiyya na tsawon makonni.

Lamarin ya tayar da hankali kan tsaro a filayen jirgin sama a Nijeriya da yadda masu aikata laifuka ke amfani da fasinjoji marasa laifi.

Hukumar ta ce za a ɗauki ƙarin matakai don hana faruwar irin wannan lamari.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • NECO ta saki sakamakon jarabawar 2025
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya
  • Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki