Aminiya:
2025-07-30@23:34:10 GMT

Hajjin 2023: An dawo wa mahajjata 3,000 kuɗaɗensu a Kaduna

Published: 3rd, February 2025 GMT

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kaduna, ta bayyana cewa sama da mahajjata 3,000 da suka yi aikin Hajjin 2023 sun karɓi ragowar kuɗinsu da ya yi saura.

Mai magana da yawun hukumar, Malam Yunusa Abdullahi ne, ya bayyana hakancikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar a Kaduna.

’Yan sanda sun ceto mutum 23 da aka sace a Kaduna Arsenal ta yi sukuwar salla a kan Man City da ci 5

Ya ce hukumar ta karɓo kuɗaɗen daga Hukumar Hajji ta Ƙasa (NAHCON).

Ya ce kowanne mahajjaci ya samu Naira 61,080.

Ya kuma ce an tura wa kuowa kuɗinsa kai-tsaye zuwa asusun bakinsu.

“NAHCON ta mayar da waɗannan kuɗaɗen ne saboda matsalar katsewar wutar lantarki da ta faru a Mina, wanda ya shafi sanyaya wuraren kwana kuma ya haifar wa mahajjata tsaiko,” in ji shi.

Abdullahi, ya ce akwai wasu da ba su karɓi kuɗinsu ba saboda rashin bayar da cikakkun bayanan asusun bankinsu.

Ya bayyana cewa biyan zagaye na biyu zai fara a mako mai zuwa, don haka ya buƙaci waɗanda ba su karɓi kuɗinsu ba da su gaggauta bahar da cikakken bayani domin samun kuɗinsu a kan lokaci.

Ya kuma jaddada cewa dukkanin mahajjatan 2023 da ba su karɓi kuɗinsu ba, su tuntubi jami’an rajista a ofisoshin ƙananan hukumominsu domin ƙarin bayani.

Hakazalika, ya ce yayin da ake ci gaba da biyankuɗaɗen na 2023, hukumar ta fara shirye-shiryen aikin Hajjin bana.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: ɗauke wuta

এছাড়াও পড়ুন:

Tsohon Ɗan Takarar Mataimakin Gwamnan Kaduna Na PDP Ya Koma ADC

Sai dai ya gode wa PDP bisa damar da ta ba shi ya tsaya takara a 2023, amma yanzu lokaci ya yi ne da zai yi gaba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa
  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati
  • Kwamandan NDA Ya Bukaci Dalibai Su Dage da Karatu a Taron FGC Malali
  • Kwamitin Aikin Hajjin 2025 Na Jihar Kano Ya Kammala Rahoton Aikinsa Na Wucin Gadi
  • Kwale-kwale Ya Kife Da Fasinjoji 16 A Karamar Hukumar Taura
  • Tsohon Ɗan Takarar Mataimakin Gwamnan Kaduna Na PDP Ya Koma ADC
  • Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci
  • SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai