HausaTv:
2025-08-01@10:43:59 GMT

Iran Ta Samu Ci Gaba A Kowane Fanni A Cikin Shekaru 40

Published: 2nd, February 2025 GMT

Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran, Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya yaba da ci gaban da Iran ta samu a fagage daban-daban, yana mai cewa kasar ta samu bunkasa a dukkan bangarori cikin shekaru 40 da suka gabata.

Iran ta yau ba Iran ce ta shekaru 40 da suka gabata ba – mun ci gaba ta kowane fanni,” in ji shi.

Jagoran ya jaddada cewa “Abin da ya bambanta Iran da sauran al’ummomi da yawa shi ne jajircewar mutanen kasar na yin Allah wadai da Amurka a matsayin mai zalunci, makaryaciya, mayaudariya da girman kai.”

Jagoran ya bayyana hakan ne a wata ganawa yau Lahadi tare da mahardatan musabaka ta Al’kur’ani mai tsarki karo na 41 da aka gudanar a Tehran babban birnin kasar Iran.

Har ila yau Ayatullah Khamenei ya jinjinawa irin sadaukarwar da kungiyoyin gwagwarmayar Falastinawa suke yi kan gwamnatin Isra’ila.

“In Allah ya yarda, Gaza za ta yi galaba a kan gwamnatin Sahayoniya,” in ji shi.

Ayatullah Khamenei ya jaddada nasarar da al’ummar Gaza suka samu kan gwamnatin sahyoniyawa da gwamnatin Amurka a matsayin misali na tabbatar da abin da ake ganin ba zai taba yiwuwa ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya karɓi baƙuncin ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin Kiru da Bebeji na Jihar Kano, Abdulmumin Jibrin Kofa.

Aminiya ta ruwaito cewa Kofa, wanda makusanci ne ga jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, kuma ɗaya daga cikin jiga-jigai a jam’iyyar NNPP, ya ziyarci shugaban ƙasar ne a yau Laraba.

Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya Tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa har zuwa baɗi — IMF

Har yanzu dai babu wasu bayanai dangane da abin da suka tattauna, amma ziyarar wadda hadimai daga ɓangarorin biyu suka riƙa yaɗawa na ci gaba da ɗaukar hankalin jama’a.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin
  • Osimhen Ya Kammala Komawa Galatasaray
  • Shugaban Kasar Iran Zai Ziyarci Pakistan A Gobe Asabar
  • Mun ci ribar Naira biliyan 414 a cikin wata 6 a Najeriya – Kamfanin MTN
  • Gwamnatin Jigawa ta horas da malamai 20,000 fasahar sadarwar zamani
  • Dalilan Da Suka Sa Canada Ta Goyi Bayan Kafa Kasar Falasɗinu
  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  •  Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta