Iran Ta Samu Ci Gaba A Kowane Fanni A Cikin Shekaru 40
Published: 2nd, February 2025 GMT
Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran, Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya yaba da ci gaban da Iran ta samu a fagage daban-daban, yana mai cewa kasar ta samu bunkasa a dukkan bangarori cikin shekaru 40 da suka gabata.
Iran ta yau ba Iran ce ta shekaru 40 da suka gabata ba – mun ci gaba ta kowane fanni,” in ji shi.
Jagoran ya jaddada cewa “Abin da ya bambanta Iran da sauran al’ummomi da yawa shi ne jajircewar mutanen kasar na yin Allah wadai da Amurka a matsayin mai zalunci, makaryaciya, mayaudariya da girman kai.”
Jagoran ya bayyana hakan ne a wata ganawa yau Lahadi tare da mahardatan musabaka ta Al’kur’ani mai tsarki karo na 41 da aka gudanar a Tehran babban birnin kasar Iran.
Har ila yau Ayatullah Khamenei ya jinjinawa irin sadaukarwar da kungiyoyin gwagwarmayar Falastinawa suke yi kan gwamnatin Isra’ila.
“In Allah ya yarda, Gaza za ta yi galaba a kan gwamnatin Sahayoniya,” in ji shi.
Ayatullah Khamenei ya jaddada nasarar da al’ummar Gaza suka samu kan gwamnatin sahyoniyawa da gwamnatin Amurka a matsayin misali na tabbatar da abin da ake ganin ba zai taba yiwuwa ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya karɓi baƙuncin ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin Kiru da Bebeji na Jihar Kano, Abdulmumin Jibrin Kofa.
Aminiya ta ruwaito cewa Kofa, wanda makusanci ne ga jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, kuma ɗaya daga cikin jiga-jigai a jam’iyyar NNPP, ya ziyarci shugaban ƙasar ne a yau Laraba.
Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya Tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa har zuwa baɗi — IMFHar yanzu dai babu wasu bayanai dangane da abin da suka tattauna, amma ziyarar wadda hadimai daga ɓangarorin biyu suka riƙa yaɗawa na ci gaba da ɗaukar hankalin jama’a.