Aminiya:
2025-08-05@14:21:47 GMT

Matasa 150 Sun Halarci Gasar Kirkire-Kirkiren Fasaha a Kano

Published: 1st, February 2025 GMT

Aƙalla matasa 150 masu kirkire-kirkire daga yankin Arewa sun hallara a Kano don halartar “Innovate North” Business Development and Innovation Hackathon, wani shiri da ke da nufin ƙarfafa harkokin kasuwanci da sauya fasalin dijital.

Yayin da take jawabi a taron, Maryam Lawan Gwadabe, wacce ta shirya gasar kuma ita ce wanda ta kafa Blue Sapphire Hub, ta jaddada mahimmancin shiryawa da ba da jagora ga matasa domin bunkasa basirarsu.

APC ta kori tsohon Gwamnan Osun, Aregbesola daga jam’iyyar Yadda Khalifan Sheikh Ibrahim Inyass ya yi wa Tinubu addu’ar nasara

“Yawancin matasa masu kirkire-kirkire ba su da jagora ko kuma wanda zai taimaka musu su sauya tunaninsu zuwa kasuwanci mai ɗorewa,” in ji ta.

Gwadabe ta bayyana gasar a matsayin babbar dama da ke bai wa matasa ‘yan Najeriya zarafin nuna fasaharsu a fannin kimiyya, fasaha da kirkire-kirkire.

Gasar ta ƙunshi kungiyoyi 30 — kowacce tana da mutum biyar, inda suka nuna basirarsu a bangaren dijital da kasuwanci a cikin yanayi na gasa.

Da yake wakiltar Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, Kwamishinan Kimiyya, Fasaha da Kirkire-kirkire, Yusuf Kofar Mata, ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar na da cikakken shirin tallafa wa matasa a fannin kirkire-kirkire da fasahohin zamani.

Ya bayyana cewa gwamnati na da shirin horar da mutum miliyan ɗaya a fannin fasahar sadarwa ta ICT kafin ƙarshen wa’adin mulkinsu.

“Abin alfahari ne ganin matasa maza da mata suna bada gudunmawa a fannin kirkire-kirkire na zamani.

“Gwamnatin Jihar Kano za ta ci gaba da tallafa musu, kuma Mai Girma Gwamna Abba Kabir Yusuf na da shirin ciyar da wannan fanni gaba cikin shekara guda,” in ji Kofar Mata.

Ya kuma jaddada cewa fasahohin zamani na da gagarumin tasiri a tattalin arziki, inda ya buƙaci matasa su yi amfani da fasaha ta hanyoyin da za su amfane su, tare da cin moriyar damar da ke cikin ɓangaren ICT.

“Kafin ƙarshen wannan wa’adin mulki, muna da shirin horar da mutum miliyan ɗaya da fasahar dijital, domin su sami abin dogaro da kansu tare da bada gudunmawa wajen ci gaban Kano da Najeriya gaba ɗaya,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arewa Jihar Kano Maryam Gwadabe

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Kano Ya Kaddamar da Shirin Dashen Bishiyoyi

Gwamnatin jihar Kano ta jaddada kudirinta na yaki da gurbacewar kasa, zaizayar kasa da sauran kalubalen muhalli.

 

 

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana hakan ne a yayin bikin kaddamar da wani katafaren shirin dashen itatuwa, inda za a dasa itatuwa miliyan 5 da rabi a fadin jihar, wanda aka gudanar a karamar hukumar Makoda.

 

 

 

Ya ce babban makasudin wannan shirin shi ne a magance dimbin kalubalen muhalli da ke addabar al’ummar jihar Kano.

 

 

Gwamna Yusuf ya jadadda cewa wadannan kalubalen na haifar da babbar matsala ga al’umma.

 

 

Gwamnan ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar ta bayar da duk wani tallafin da ya dace don shayar da ‘ya’yan itatuwan, ta yadda za su yi girma da kuma cim ma burin da aka yi niyya. Wannan tallafi yana da mahimmanci don nasarar shirin.

 

 

Ya bukaci dukkan shugabannin kananan hukumomi 44, shugabannin gargajiya, da jami’an ci gaban al’umma (CDOs) da su sanya hannu a cikin wannan shirin, inda ya ce shigar su na da matukar muhimmanci wajen cimma manufofin shirin.

 

“Idan aka kula da kyau itatuwan da aka dasa ta wannan shiri za su taka rawar gani wajen magance sauyin yanayi da batutuwan da ke da alaka da hakan. Hakan ya yi dai-dai da manyan manufofin jihar Kano.”

 

Kwamishinan Muhalli, Dr. Dahiru Mohammad Hashim, ya yaba da kudurin Gwamna Yusuf na tallafawa kokarin ma’aikatar wajen dakile matsalolin muhalli.

 

Sarkin Dawakin Mai Tuta Alhaji Mohammad Bello Abubakar, wanda ya wakilci Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Muhammad Sanusi II ya jaddada goyon bayan Masarautar kan shirin dashen itatuwa.

 

 

Taron ya gabatar da bayar da kyautuka ga mutanen da suka bayar da gudunmawa sosai wajen tallafawa al’ummarsu.

 

 

Wannan amincewa yana aiki azaman abin ƙarfafawa ga wasu don shiga cikin ayyukan muhalli.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sashen Lafiya Zai Fara Amfani Da Sabuwar Fasahar AI Don Inganta Lafiya
  • Gwamna Yusuf Ya Raba takardun daukar Aiki Ga Sabbin Ma’aikatan Gona Su 1 ,038
  • Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 
  • Gwamna Yusuf Ya Kaddamar da Shirin Dashe Itatuwa Don Yaki da Matsalolin Muhalli
  • Gwamnan Jihar Kwara Ya Hori Sabbin Matasa Masu Yiwa Kasa Hidima Akan Kishin Kasa
  • Gwamnan Kano Ya Kaddamar da Shirin Dashen Bishiyoyi
  • Sauyin Yanayi: Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da shirin dashen bishiya miliyan 5
  • Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ
  • Mutum ɗaya ya rasu, an jikkata wasu yayin arangama da ’yan sanda a Abuja
  • Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya