Jami’in Kenya: Fasahar Sin Na Ingiza Samar Da Wutar Lantarkin Kenya
Published: 1st, February 2025 GMT
Kasar Kenya na amfani da damar ci gaban fasahar kasar Sin don kara dogaro da samar da wutar lantarki a kasar.
Darektan ma’aikatar kula da harkokin rarraba wutar lantarki ta kasar Joseph Siror ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a, inda ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua a Nairobi, babban birnin kasar Kenya cewa, ababen more rayuwa a fannin samar da wutar lantakin kasar na kunshe da dimbin kayayyakin aiki daga kamfanonin kasar Sin irin su Huawei da rukunin Yocean.
“Sashen wutar lantarki na Kenya ya kuma ci moriyar musayar fasaha da kara sanin makamar aiki daga kamfanonin kasar Sin,” kamar yadda Siror ya bayyana a lokacin da kamfanin ya fitar da sakamakon rabin shekarar da ta gabata a ranar 31 ga Disamban 2024.
Siror ya kara cewa, masana’antun kasar Sin da dama sun yi nasara a takarar neman samar wa ma’aikatar wutar lantarki ta Kenya da na’urorin wutar lantarki saboda ci gaban fasaharsu da kuma karfi a bangaren hada-hadar kudi. Ya jaddada cewa, ta hanyar hadin gwiwa da kamfanonin kasar Sin, kasar Kenya ta samu damar samun hanyoyin samun kayayyakin wutar lantarki masu inganci kuma na zamani, da tsarin rarraba makamashi mai inganci, da na’urorin tantance yawan amfani da lantarki na zamani. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)
কীওয়ার্ড: wutar lantarki
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
A nasa ɓangaren, mai bai wa Gwamnan Shawara Kan Al’ammuran Tsaro, Janar Dahiru Abdusalam (Mai Ritaya), ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar tana ɗaukar matakai tare da jami’an tsaro don samar da tsaro mai inganci.
Ya kuma bayyana cewa duk da matsalolin tsaro da ake fuskanta a hanyar Damaturu zuwa Gujba, jami’an tsaro na ƙoƙarin yin sintiri domin tabbatar da tsaro.
Janar Dahiru ya ce, “Koda yake muna fuskantar ƙalubale daga Boko Haram a yankunan wasu sansanin sojoji, jami’an tsaro na ci gaba da aikinsu domin kare yankin.”
Ya ƙara da cewa, “Muna taka-tsan-tsan musamman wajen daƙile karɓar haraji daga Boko Haram a wasu yankuna. Wannan al’amari yana da matuƙar wahala, amma muna fatan za mu samu nasara.”
Janar Dahiru ya tabbatar da cewa akwai tsaro a dukkanin sassan jihar tare da haɗin gwiwar sojoji, ‘yansanda, Civilian JTF da ‘yan sa-kai.
Ya kuma bayyana cewa za a fitar da sabbin dabaru cikin makonni masu zuwa domin yaƙar ‘yan ta’adda.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp